ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 26, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dalilin Gwamnatin Tarayya Na Fara Aikin Gina Mayankar Zamani A Garin Jos

by Abubakar Abba
50 minutes ago
Mayanka

A ƙoƙarinta na zamanantar da Mayankar dabbobi da ƙara bunƙasa fannin gwamnatin tarayya, ta fara aikin gina katafariyar mayankar da za a iya yanka Shanu kimanin 500 a kowace rana.

Babban Ministan Ma’aikatar Bunƙasa Kiwon DabbobiIdi, Mukhtar Maiha, ya sanar da haka ne a jawabinsa, yayin ƙaddamar da aikin a Jihar Filato.

Ya danganta aikin a matsayin wanda zai taimaka wajen zuba jari a fannin da ƙara samar da wadataccen abinci da kuma samar da aikin yi ga fannin na kiwon wannan ƙasa.

ADVERTISEMENT

Maiha ya sanar da cewa, Mayankar za ta samar da tsarin sarrafa Nama na zamani, inda hakan zai yi daidai da yadda ake gudanarwa a faɗin duniya.

Ya ƙara da cewa, tsarin zai kuma ƙara taimaka wa gwamnatin tarayya, kan ƙoƙarin da ta ke yin a ci gaba da haɓaka fannin na kiwon dabbobi a ɗaukacin faɗin ƙasar.

LABARAI MASU NASABA

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa

Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA

A cewarsa, wannan aikin ana sa ran, zai samar da ayyukan yi na kai tsaye, da waɗanda ba na kai tsaye ba daga tsakanin 7,000 zuwa 10,000 a ɗaukacin fannin na kiwon dabbobi a ƙasar nan.

Ya ci gaba da cewa, aikin zai kuma ƙara inganta duba lafiyar dabbobi da jigilar Naman da aka sarrafa na dobbobin, musamman ta hanyar sanya Naman a cikin na’urar sanyi ta zamani tare da kuma ƙara samar Ƙiraza.

Kazalika, a Mayankar za a rinƙa sarrafa ƙashin dabbobi da Jininsu da ƙasusuwansu da sauran makamantansu, inda za a sarrafa su, domin sayarwa.

Ministan ya bayyana cewa, an zaɓo Jihar Filato domin gudanar da aikin ne, duba da cewa; ta kasance ingantacciyar ƙasar yin noma mai kyau tare da mayar da hankali a ɓangren kiwo, musamman na dabbobi.

Ya yi nuni da cewa, Filato ta kuma kasance tana da kyakkyawan yanayi tare da kuma kasancewa cibiyar gudanar da bincike kan lafiyar dabbobi, wato NƁRI da ke a Ɓom.

A nasa jawabin, gwamnan jihar ta Filato, Caleb Mutfwang, ya danganta wannan haɗakar a tsakanin gwamnatin tarayya da kuma ma’aikatar kula da kiwon dabbobi ta tarayya, a matsayin wani mataki na amfana da fannin na kiwon dabbobi.

Mutfwang, wanda aka wakilce shi a wajen taron ya bayyana cewa, Filato na goyon bayan yin amfani da Ruga ta zamani, musamman domin a ƙara bunƙasa fannin kiwon dabbobi a ɗaukacin faɗin jihar tare da ƙara haɓaka fannin tattalin arziƙin jihar.

Shi kuwa a nasa jawabin, Jami’i na ƙasa mai kula da shirin bunƙasa kiwon dabbobi da tallafawa iyalai (L-PRES), Dakta Sanusi Abubakar, ya sanar da cewa; Mayankar ta kai mataki na duniya, musamman wajen samar da ingantacce kuma tsaftattacen Nama.

Ya ƙara da cewa, Mayankar za ta kuma taimaka wajen janyo hankalin masu zuba jari tare da ƙara ƙarfafa fannin kiwon dabbobi na ƙasar.

A cewarsa, Bankin Duniya ne ya taimaka wa aikin, wanda kuma Gwamnatin Jihar Filato, za ta wanzar da shi.

 Ya ce, idan an kammala aikin, ana sa ran zai kasance wanda sauran yankunan da ke maƙwabtaka da Filato, su ma za su amfana da shi, musamman wajen adana Nama da kuma rabar da shi ko tura shi zuwa gurare daban-daban.

Mayanka
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Kotu Ba Ta Da Hujjar Umartar INEC Ta Soke Rajistar Jam’iyyu —Uban Doman Lafiya
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA

MASU ALAKA

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa

June 20, 2026
Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA
Noma Da Kiwo

Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA

June 20, 2026
Kungiyar Manoman Citta Ta Kasa Ta Yaba Wa Gwamnatin Tarayya Kan Tallafin Da Take Ba Su
Noma Da Kiwo

Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

June 19, 2026
Next Post
Sin Ta Habaka Karfin Soja Ne Don Kare Ikon Mallakar Kasa Da Muradun Ci Gaba

Sin Ta Habaka Karfin Soja Ne Don Kare Ikon Mallakar Kasa Da Muradun Ci Gaba

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Habaka Karfin Soja Ne Don Kare Ikon Mallakar Kasa Da Muradun Ci Gaba

Sin Ta Habaka Karfin Soja Ne Don Kare Ikon Mallakar Kasa Da Muradun Ci Gaba

June 26, 2026
Mayanka

Dalilin Gwamnatin Tarayya Na Fara Aikin Gina Mayankar Zamani A Garin Jos

June 26, 2026
Sin Ta Yi Allah Wadai Da Amfani Da Haraji Ba Bisa Ka’ida Ba Ta Fakewa Da Zargin “Kwadagon Tilas”

Sin Ta Yi Allah Wadai Da Amfani Da Haraji Ba Bisa Ka’ida Ba Ta Fakewa Da Zargin “Kwadagon Tilas”

June 26, 2026
NDC Ta Ce Za Ta Ɗaukaka Ƙara Kan Hukuncin Soke Rajistarta

NDC Ta Ce Za Ta Ɗaukaka Ƙara Kan Hukuncin Soke Rajistarta

June 26, 2026
An Fitar da Jadawalin Wasannin Zagayen Farko Na Gasar Carabao Cup ta 2026/2027

An Fitar da Jadawalin Wasannin Zagayen Farko Na Gasar Carabao Cup ta 2026/2027

June 26, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ba Ta Da Hujjar Umartar INEC Ta Soke Rajistar Jam’iyyu —Uban Doman Lafiya

June 26, 2026
Xi Ya Mika Jaje Kan Mummunar Girgizar Kasar Venezuela

Xi Ya Mika Jaje Kan Mummunar Girgizar Kasar Venezuela

June 26, 2026
Gwamnatin Tarayya, Bankin Duniya Da Cibiyar IITA Za Su Bunkasa Noma Ta Fasahar Zamani

Bankin Duniya Ya Ɗora Tashoshin Apapa Da Tincan Kan Sikelin Maki Na 20 A Duniya

June 26, 2026
sikila

Buƙatar Mayar Da Hankali Wajen Kawo Ƙarshen Ciwon Sikila A Nijeriya

June 26, 2026
Sin Ta Bankado Laifukan Miyagun Kwayoyi 12,000 A Watanni Biyar Na Farkon Bana

Sin Ta Bankado Laifukan Miyagun Kwayoyi 12,000 A Watanni Biyar Na Farkon Bana

June 26, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.