A ƙoƙarinta na zamanantar da Mayankar dabbobi da ƙara bunƙasa fannin gwamnatin tarayya, ta fara aikin gina katafariyar mayankar da za a iya yanka Shanu kimanin 500 a kowace rana.
Babban Ministan Ma’aikatar Bunƙasa Kiwon DabbobiIdi, Mukhtar Maiha, ya sanar da haka ne a jawabinsa, yayin ƙaddamar da aikin a Jihar Filato.
Ya danganta aikin a matsayin wanda zai taimaka wajen zuba jari a fannin da ƙara samar da wadataccen abinci da kuma samar da aikin yi ga fannin na kiwon wannan ƙasa.
Maiha ya sanar da cewa, Mayankar za ta samar da tsarin sarrafa Nama na zamani, inda hakan zai yi daidai da yadda ake gudanarwa a faɗin duniya.
Ya ƙara da cewa, tsarin zai kuma ƙara taimaka wa gwamnatin tarayya, kan ƙoƙarin da ta ke yin a ci gaba da haɓaka fannin na kiwon dabbobi a ɗaukacin faɗin ƙasar.
A cewarsa, wannan aikin ana sa ran, zai samar da ayyukan yi na kai tsaye, da waɗanda ba na kai tsaye ba daga tsakanin 7,000 zuwa 10,000 a ɗaukacin fannin na kiwon dabbobi a ƙasar nan.
Ya ci gaba da cewa, aikin zai kuma ƙara inganta duba lafiyar dabbobi da jigilar Naman da aka sarrafa na dobbobin, musamman ta hanyar sanya Naman a cikin na’urar sanyi ta zamani tare da kuma ƙara samar Ƙiraza.
Kazalika, a Mayankar za a rinƙa sarrafa ƙashin dabbobi da Jininsu da ƙasusuwansu da sauran makamantansu, inda za a sarrafa su, domin sayarwa.
Ministan ya bayyana cewa, an zaɓo Jihar Filato domin gudanar da aikin ne, duba da cewa; ta kasance ingantacciyar ƙasar yin noma mai kyau tare da mayar da hankali a ɓangren kiwo, musamman na dabbobi.
Ya yi nuni da cewa, Filato ta kuma kasance tana da kyakkyawan yanayi tare da kuma kasancewa cibiyar gudanar da bincike kan lafiyar dabbobi, wato NƁRI da ke a Ɓom.
A nasa jawabin, gwamnan jihar ta Filato, Caleb Mutfwang, ya danganta wannan haɗakar a tsakanin gwamnatin tarayya da kuma ma’aikatar kula da kiwon dabbobi ta tarayya, a matsayin wani mataki na amfana da fannin na kiwon dabbobi.
Mutfwang, wanda aka wakilce shi a wajen taron ya bayyana cewa, Filato na goyon bayan yin amfani da Ruga ta zamani, musamman domin a ƙara bunƙasa fannin kiwon dabbobi a ɗaukacin faɗin jihar tare da ƙara haɓaka fannin tattalin arziƙin jihar.
Shi kuwa a nasa jawabin, Jami’i na ƙasa mai kula da shirin bunƙasa kiwon dabbobi da tallafawa iyalai (L-PRES), Dakta Sanusi Abubakar, ya sanar da cewa; Mayankar ta kai mataki na duniya, musamman wajen samar da ingantacce kuma tsaftattacen Nama.
Ya ƙara da cewa, Mayankar za ta kuma taimaka wajen janyo hankalin masu zuba jari tare da ƙara ƙarfafa fannin kiwon dabbobi na ƙasar.
A cewarsa, Bankin Duniya ne ya taimaka wa aikin, wanda kuma Gwamnatin Jihar Filato, za ta wanzar da shi.
Ya ce, idan an kammala aikin, ana sa ran zai kasance wanda sauran yankunan da ke maƙwabtaka da Filato, su ma za su amfana da shi, musamman wajen adana Nama da kuma rabar da shi ko tura shi zuwa gurare daban-daban.














