Babban jigo na jam’iyyar ADC a Jihar Nasarawa Alhaji Haruna Uban Doman Lafiya ya ce babbar kotun tarayya Abuja ba ta da hurumin ba hukumar zaɓe mai zaman kanta umarni na cewar ta soke rajistar jam’iyyu biyar da suka haɗa da ADC, Accord party, Action Alliance, Action Peoples party, da kuma Zenith Labour party, ba domin komai ba sai saboda sun gaza samun kashi 25 daga cikin 100 daga cikin zaɓukan da aka yi a baya.
Alkalin Babbar kotun tarayya Abuja a ƙarƙashin jagorancin jagorancin mai shari’a Peter Lifu, amma mai shari’a, A Muhammed na kotun ɗaukaka ƙara Abuja ya nuna matakin na Alkalin babbar kotun Abuja rashin biyayya ne ga hukuncin da kotu ta aiwatar.
Hukumar zaɓe mai zaman kanta kamar yadda ya ce hukuma ce mai zaman kanta iat ce ta yi ma jam’iyyun rajisata saboda ta ga cewra su cancanta da ayi masu rajistar a matsayin jam’iyyun siyasa. Ya ce duk kyan kotu ai tsaya take a kawo mata ƙara tukunna kafin har ta kai ga ɗaukar wani mataki.Ya ce INEC ta daɗe da kammala aikinta wajen yi ma jam’iyyun rajista.
Ya ce Shugaban ƙasa Tinubu da ƴan kanzaginsa suna tsoron jam’iyyar ADC ne saboda kuwa ta daɗe da shan gabansu, musamman ma ɗan takararta na Shugaban ƙasa Alhaji Atiku Abubakar wanda suke da shakkun yana da ɗimbin magoya bayansa da suka shafe na Tinubu.
Ya ƙara jaddada cewa a matsayin sun a ƴan Nijeriya suna iya tsayawa takara a duk jam’iyyar da suka ga dama, ba dole ba ne sai sun tsaya a ƙarƙashin jam’iyya mai mulki.
Game da ƴansandan Jihohi ya ce ba za a sakar masu mara su sakata su wala ba, domin irinsu za su riƙa kasancewa ne a ƙarƙashin umarnin Gwamnoni waɗanda dole ne sai watarana sun yi amfani da su,domin a cimma wani buri wanda na daban ne, kai ana iya ma musaguna ma waɗanda ba su jam’iyya ɗaya da gwamna. Mai ƙarfi kuma idan ba sa’a aka yi ba ƙarƙashin ƴansandan Jihar shi ne wanda zai riƙa danne wand aba shi da ƙarfi.














