ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Har Yanzu Wasu Na Yi Wa ‘Yan Fim Kallon Mutanen Banza —Auwal West

by Rabi'at Sidi Bala
3 years ago
Auwal West

Fitaccen Jarumin nan da ya shafe tsahon shekara ashirin da bakwai cikin masana’antar shirya fina-finan Hausa ta Kannywood, Jarumin da ke ci gaba da haskawa a cikin sabbin fina-finai masu dogon zangon da ke fita a yanzu AUWAL ISAH WEST, ya yi bayani dangane da abin da ya shafi rayuwarsa da kuma harkarsa ta fim. Ga dai tattaunawar tare da wakiliyarmu RABI’AT SIDI BALA kamar haka:

Ya sunan Jarumin?

Sunana Auwa Isah West.

ADVERTISEMENT

Ko za ka fadawa masu karatu dan takaitaccen tarihinka?

Ni dan asalin Jihar Kano ne, Mamata ‘yar Kura ce, Babana dan Garko Jihar Kano ne, daga bisani aiki ya kai Babana Jihar Filato. Na yi karatuna a garin Jos, bayan babana ya rasu na dawo garin Kano wajen ‘Yan’uwana. Bayan nan sai na shiga harkar fim dalilin Ali Nuhu shi ne maigida na.

LABARAI MASU NASABA

Zan Iya Auren Namiji Komai Talaucinsa Muddin Muna Son Junanmu -Maryam Labarina

Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi

Me ya ja hankalinka har ka tsunduma harkar fim

Eh! Toh, ina sha’awar abun ne kawai.

Ya gwagwarmayar shiga masana’antar ta kasance?

Ban sha wata wahala ba, saboda ina da maigidana Ali Nuhu kuma ta dalilinsa na shiga.

Za ka yi kamar shekara nawa da fara fim?

Zan kai kamar shekara Ashirin da bakwai (27) da farawa.

Ko akwai wani kalubale daka fuskanta wajen iyaye, musamman lokacin daka fara sanar musu kana son shiga masana’antar?

Allahamdulillah ban taba samun wani kalubale ba ‘because I’m the best’.

A wanne fim ka fara fitowa?

Na fara da fim din Zubaida.

Da wanne Jarumi da Jaruma kuka fito cikin fim din, kuma wanne rawa ka taka cikin fim din, kuma ya karbuwar fim din ta kasance?

Na fito tare da Ahmad S.Nuhu da sarki Ali Nuhu  da Abida Muhammad. Gaskiya fim din ya samu karbuwa sosai a kasuwa.

Bayan da ka samu nasarar shiga cikin masana’antar, wanne irin kalubale ka fara cin karo da shi?

Toh! gaskiya ban samu wani kalubale ba, because ni na zo da zuciya daya, kuma Allah ya bani sa’a saboda na dauke ta sana’a, sabanin wasu ba haka suka dauka ba.

Bayan da ka shafe tsawon shekaru fa, ko akwai wani kalubale da ka taba fuskanta?

Akwai gaskiya, wasu ba su dauke mu a matsayin wasu mutane kamar kowa ba, ‘Sometimes’ ma in mun je neman aure iyayen yaran suna mana ganin mutanen banza, shi ne kawai.

Wadanne irin nasarori ka samu game da fim?

Na samu nasarori sosai ina gode wa Allah, kuma ina gode wa maigidana Ali Nuhu.

Ya ka dauki fim a wajenka?

Na dauki fim babbar sana’a, duk abin da na samu a rayuwata daliln fim ne, so ina mai gode wa Allah sosai.

Me kake son cimmawa game da fim?

Ina fatan nima in samu wani dama da zan taimaki wasu kamar yadda aka yi min.

Bayan fim kana wata sana’ar ne?

Ina harkar mota, kuma ina da shagon kaya.

Kwanakin baya can masu kallo sun daina jin duriyarka, daga bisani kuma kwatsam sai ga shi ka dawo a wannan lokacin, me ya faru?

Toh! Dalilin hakan na je karo ilmi a ‘South Africa’ ne shiyasa.

Da yawan fina-finan da kake fitowa, ka fi fitowa a dan daba, wanda hakan ke sa wasu mutanen ke yi maka mummunan kallo, shin kai kake zabar hakan, ko kuwa labari ne ya ke zabarka?

Gaskiya ba haka bane, ba ni nake zabar hakan ba, labari ne yake zuwa da haka amma ina jin dadin hakan.

Ko za ka iya tuna adadin fina-finan da ka yi?

Gaskiya suna da yawa ba zan iya tunawa ba.

A gaba daya fina-finan da kayi wanne fim ka fi so, wanda ya zamo bakandamiyarka?

Kowanne fim ina so, amma na fi san ALAKA fim din Maigidana Ali Nuhu.

Bayan fitowa da kake matsayin Jarumi, shin kana rubuta labari, ko Bada umarni, ko shiryawa da sauransu, ko iya aktin kawai kake yi?

Eh! toh ina acting da kuma products.

Da wanne Jarumi ko Jaruma ka fi so a hada ka a fim kuma me ya sa?

Gaskiya ina jin dadin aiki da kowa, amma na fi jin dadin aiki da maigidana Ali Nuhu ‘because he’s so nice’.

Wanne abu ne ya taba faruwa da kai na farin ciki ko akasin hakan, wanda ba za ka taba iya mantawa da shi a rayuwa ba?

Gaskiya akwai, mun taba zuwa Katsina ni da maigidana Ali Nuhu gidan wata mata take cewa “Ali mai ya hada ka da wannan mugun, ya bata ma shiri…”, sai oga na ya ce “ai fim ne Hajiya shi din na hannun damana ne” kuma ya kara da cewa ya fi sona a duk yaransa.

Ya batun aure, shin akwai ko kuma tukunna dai?

Eh! ina da aure yarana biyu Mace da Mamiji na yi wa ogana Ali Nuhu takwara.

Idan na fahimce ka a cikin masana’antar Kannywood Ali Nuhu shi ne ubangidanka, kamar yadda kowa ya ke da ubangida?

Eh! Sosai ma har ya wuce matsayin Ubangida masayin uba yake a guna shi ne Sarki Ali Nuhu.

Wanne irin matsaloli kuka fi fuskanta a cikin masana’antar, kuma ta wacce hanya kake ganin za a bi a gyara?

Rashin hadin kai da raina na gaba da kai. Eh! toh, kira na anan shi ne, mu ruke juna kuma mu ji tsoran Allah a duk inda muke, mu sani mu wakilan al’umma ne.

Mene ne burinka na gaba game da fim?

Burina game da fim bai wuce na Allah ya bani sa’a ni ma in rinka fim na kaina ba.

Wanne kira za ka yi ga masu kokarin shiga cikin masana’antar har ma da wadanda suke ciki?

Toh su yi hakuri saboda akwai wahala, so dole sai sun yi hakuri.

Me za ka ce ga makaranta wannan shafi na RUMBUN NISHADI?

Ina yi wa kowa fatan alkhairi da wannan gidan Jarida Allah ya sa ku fi haka.

Me za ka ce da ita kanta Jaridar Leadership Hausa?

Toh ina mai godiya da wannan dama da kuka bani ina muku fatan alkhairi Allah ya sa kufi haka.

Ko kana da wadanda za ka gaisar?

Ina gaida kowa da kowa masoyana na duniya gabaki daya.

Muna godiya ayi sallah lafiya

Ni ma na gode.

Auwal West
Rabi'at Sidi Bala
+ postsBio
  • Rabi'at Sidi Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiat-sidi-bala/
    Zan Iya Auren Namiji Komai Talaucinsa Muddin Muna Son Junanmu -Maryam Labarina
  • Rabi'at Sidi Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiat-sidi-bala/
    Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi
  • Rabi'at Sidi Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiat-sidi-bala/
    Bukatar Rike Sirri A Tsakanin Ma’aurata
  • Rabi'at Sidi Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiat-sidi-bala/
    GORON JUMA’A

MASU ALAKA

Zan Iya Auren Namiji Komai Talaucinsa Muddin Muna Son Junanmu -Maryam Labarina
Nishadi

Zan Iya Auren Namiji Komai Talaucinsa Muddin Muna Son Junanmu -Maryam Labarina

June 14, 2026
Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi
Nishadi

Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi

June 14, 2026
Ban Taɓa Fitowa A Fim Na Yi Da-na-sani Ba —Habibu Yaro
Nishadi

Ban Taɓa Fitowa A Fim Na Yi Da-na-sani Ba —Habibu Yaro

May 31, 2026
Next Post
Karen Da Ya Fi Kowanne Tsufa A Tarihin Duniya

Karen Da Ya Fi Kowanne Tsufa A Tarihin Duniya

LABARAI MASU NASABA

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.