ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Karen Da Ya Fi Kowanne Tsufa A Tarihin Duniya

by Rabi'u Ali Indabawa
3 years ago
Duniya

Wani kare a kasar Portugal ya zama wanda ya fi ko wanne kare shekaru a tarihin duniya, ya karta tarihin da aka shafe sama da shekara 100 da kafawa in ji – Guinness World Records.

Bobi na cikin jinsin karnukan Rafeiro do Alentejo – da a rayuwa ba sa wuce shekara 12 zuwa 14.

  • Shawarar Kasar Sin Game Da Tsaron Kasa Da Kasa Ta Ingiza Zaman Lafiya Da Daidaito A Duniya, In Ji Masana
  • Abin Da Ya Zama Wajibi Manoman Rogo Su Yi Don Samun Amfani Mai Yawa

Karen da a baya yake rike da wannan tarihi shi ne Bluey da ke Australia, wanda ya mutu a 1939 yana da shekaru 29 da wata biyar a raye.

ADVERTISEMENT

Ranar 1 gawatan Fabirairu Bobi ya cika shekara 30 da kwana 226, kuma yana yin abin duk da ake so a wannan shekarun nasa.

An tabbatar da shekarun nasa ne ta hannun gwamnatin Portugal karkashin kulawar Hukumar Kula da Dabbobi ta kasar, kamar yadda Guinness World Records ta bayyana.

LABARAI MASU NASABA

Ana Zargin Jami’in Kwastam Da Kashe Kansa A Bauchi Saboda Damuwa

EFCC Ta Cafke Lauyan Bogi Da Mallakar Hatimin Kungiyar Lauyoyi Ta Nijeriya Na Jabu A Legas

Ya na zaune da iyalan Costa a kayen Conkueiros a duk tsayin rayuwarsa, da suke zaune a gabar tekun Portugal, kuma yana da ‘yan uwa uku da mahaifiyarsa ta haifa.

Leonel Costa, wanda shekararsa takwas a lokacin, yace mahaifansa na da dabbobin da suke kiwo da dama, don haka suka yasar da wasu da yawa sai dai Bobi ya tsallake rijiya da baya.

Leonel da dan uwansa sun rika boye Bobi suna ci gaba da kiwonsa, har sai lokacin da ya zama wani bangare na gidansu, wanda yake ba shi abinci irin wanda suke ci.

“Tsakanin abincin gwangwani na dabbobi da nama, Bobi bai fiye damuwa ya ci ko daya ba, ya fi damuwa ya ci irin abin da muke ci, in ji Mista Costa, wanda ko da yaushe yake neman abincinsa cikin ruwa.

Bayan wata rashin lafiya da ya yi a 2018 har aka kwantar da shi a asibiti saboda gaza numfashi da ya yi, Mista Costa ya ce kare na rayuwa ne cikin kwanciyar hankali, kuma sirrin tsayin rayuwarsa shi ne “nutsuwa da samun muhallin da ke cike da zaman lafiya” da yake rayuwa cikinsa.

Kuma kamar gado ya yi daga wajen mahaifiyarsa, mahaifiyar Bobi sai da ta yi shekara 18 a raye.

Amma duk da haka, lokaci na neman cimma Bobi, domin yanzu yana da matsalar kafa da kuma gani.

Costa ya ce Bobi shi ne “na karshe a tsarin dabbobin” a gidanmu kuma ya ce “shi din na daban ne.”

Nadin da aka yi wa Bobi na karen da ya fi dadewa a duniya na zuwa ne mako biyu bayan Guinness World Records ta nada wani kare Spike the Chihuahua, mafi dadewa a raye wanda ya kwashe shekara 23 a raye.

Amma bayan nan sai kungiyar ta sauya tarihin ta sanar da Bobi a matsayin karen da ya fi dadewa a duniya.

Duniya
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijar Ta Rattaba Hannu A Kan Dokar Haramta Auren Jinsi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Za Mu Iya Sayar Da Manmu Ba Tare Da Wata Matsala Ba -Iran
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Dattawan Arewa Sun Buƙaci Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Tabarbarewar Tsaro
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijeriya Ta Karbi Ƴan Nijeriya 268 Da Suka Tsero Daga Afirka Ta Kudu

MASU ALAKA

Ana Zargin Jami’in Kwastam Da Kashe Kansa A Bauchi Saboda Damuwa
Al'ajabi

Ana Zargin Jami’in Kwastam Da Kashe Kansa A Bauchi Saboda Damuwa

June 9, 2026
EFCC Ta Cafke Lauyan Bogi Da Mallakar Hatimin Kungiyar Lauyoyi Ta Nijeriya Na Jabu A Legas
Al'ajabi

EFCC Ta Cafke Lauyan Bogi Da Mallakar Hatimin Kungiyar Lauyoyi Ta Nijeriya Na Jabu A Legas

April 21, 2026
Yadda Aka Gano Ƙasusuwan Dabba Mai Shekara Miliyan 100 A Nijar
Al'ajabi

Yadda Aka Gano Ƙasusuwan Dabba Mai Shekara Miliyan 100 A Nijar

March 8, 2026
Next Post
Gini 10 Mafiya Darajar Kudi A Fadin Duniya

Gini 10 Mafiya Darajar Kudi A Fadin Duniya

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.