ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Harin Iran: Amurka Da Isra’ila Sun Bata Lissafi

by CGTN Hausa and Sulaiman
4 months ago
Iran

Amurka da Isra’ila sun kaddamar da hare-hare kan Iran ne bisa wai “wani matakin da ya dace don kawar da barazana.” Amma da yawa manazarta da suka san yankin Gabas ta Tsakiya da kuma musamman tarihin kasar Iran mai shekaru sama da 2000 da kafuwa, suna ganin cewa harin na iya zama kuskure ko batan lissafi, bisa tunanin yadda sakamakon da zai biyo baya na iya daukar tsawon shekaru ta fuskar zaman lafiya, matsin lambar diflomasiyya, da kuma kara hadarin matsalar tsaro.

Masu lura da al’amura sun lura cewa daya daga cikin manya-manyan kura-kurai shi ne tunanin cewa matakin soji zai raunana tsarin siyasar Iran. A maimakon haka, da alama harin ya karfafa ikon hukumomin Iran bisa kara dankon hadin kai a tsakaninsu da mabambantan sassan siyasa da suke da sabanin ra’ayi, da rage damar yin sulhu da kuma karfafa muryoyin masu kishin kasa da ke kara yekuwar nuna wa al’ummar kasar cewa wannan yakin na gwagwarmayar dorewar kasar ne. Don haka, ake ganin bin hanyar diflomasiyya ta gaskiya tare da Amurka zai yi matukar wahala. Ana iya samun maslaha amma ta wucin-gadi, amma babu zancen amincewa da juna.

Wani abin damuwa da masana yankin suka nuna shi ne girman ramuwar gayyar da take biyo bayan hare-haren. Martanin Iran, wanda ya hada da harba makami mai linzami da tattaro kungiyoyin kawance a duk fadin yankin Gabas ta Tsakiya, ya nuna irin karfin da wasu manazarta ke ganin Amurka da Isra’ila suna masa kallon reni. Kuma wannan ne zai zama silar kara fadada rikicin Gabas ta Tsakiya wanda tuni ya shafi kasashe da dama, lamarin da ke kara nuna fargabar barkewar fadan da zai dade ana yi yankin. Sannan wadanda suka haddasa fitinar ba su da wata taswirar kawo karshen lamarin ko takamaimiyar hanyar siyasar da za a bi.

ADVERTISEMENT

Abubuwan da ke faruwa sun zarce batun matakin sojin da aka dauka. Masu sharhi na ganin lamarin yana da illoli ta fuskar diflomasiyya, musamman ga Isra’ila, wadda a yanzu ke fuskantar karin matsin lamba daga kasashen duniya tun daga kan kisan kiyashinta na Gaza. Ga bangaren Amurka kuma, lamarin zai iya haifar mata da tutsu daga abokan hulda da ke fargabar wargajewar tsarin samarwa a kasuwar makamashi ta duniya da kuma sauran hanyoyin kasuwancin yanki. Kazalika, daukar matakin soji zai iya zama na dogon lokaci wanda hakan zai kara karkatar da hankali da albarkatun Amurka daga wasu abubuwan da ta sa gaba a duniya, kamar cike gibin kasuwanci da sauran matsaloli na cikin gida.

Trump ya yi yakin neman zabensa da cewa ba zai tsunduma Amurka cikin yaki na dogon lokaci ba a wa’adinsa. Amma yanzu ya saba lamba, kuma har manyan ’yan siyasar Amurka masu goyon bayan kudurinsa na siyasa irin su Marjorie Taylor Greene, Thomas Massie, Rand Paul, Turker Carlson da sauransu sun yi Allah wadai da yakin na Iran.

LABARAI MASU NASABA

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Kisan jagoran addini na Iran Ayatollah Khomeini wani babban kuskure ne a cikin wannan yakin saboda ba wai kai a matakin kasar Iran yake da tasiri ba, yana da dimbin mabiya wadanda za su iya sadaukar da rayukansu a sassan duniya daban-daban wajen neman daukar fansa. Kuma matukar zuciyar dan’adam take kashe a kan wani abu, to ba a san ranar samun mafita ba.

Kamar yadda Hausawa ke yawan fada, fitina bacci take, kuma Allah ya la’anci mai tayar da ita, muna fata wannan la’ana ta tsaya kan wadanda suka tayar ba tare da sauran al’ummar da ba-ta -ji-ba-ba-ta-gani ba. (Abdulrazaq Yahuza Jere)

 

Iran
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN: Fasahohin Zamani Sun Habaka Ayyuka Yayin Da Tsarin Cin Moriya Tare Ya Yi Fintinkau
Iran
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu
  • Sulaiman
    Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani
  • Sulaiman
    Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100
  • Sulaiman
    Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

MASU ALAKA

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu
Daga Birnin Sin

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani
Daga Birnin Sin

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya
Daga Birnin Sin

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026
Next Post
Kafar CGTN Ta Fitar Da Rahoto Game Da Hasashen Ababen Mayar Da Hankali Yayin Manyan Taruka Biyu Na Sin

Kafar CGTN Ta Fitar Da Rahoto Game Da Hasashen Ababen Mayar Da Hankali Yayin Manyan Taruka Biyu Na Sin

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.