ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Harin Iran: Amurka Da Isra’ila Sun Bata Lissafi

by CGTN Hausa and Sulaiman
4 months ago
Iran

Amurka da Isra’ila sun kaddamar da hare-hare kan Iran ne bisa wai “wani matakin da ya dace don kawar da barazana.” Amma da yawa manazarta da suka san yankin Gabas ta Tsakiya da kuma musamman tarihin kasar Iran mai shekaru sama da 2000 da kafuwa, suna ganin cewa harin na iya zama kuskure ko batan lissafi, bisa tunanin yadda sakamakon da zai biyo baya na iya daukar tsawon shekaru ta fuskar zaman lafiya, matsin lambar diflomasiyya, da kuma kara hadarin matsalar tsaro.

Masu lura da al’amura sun lura cewa daya daga cikin manya-manyan kura-kurai shi ne tunanin cewa matakin soji zai raunana tsarin siyasar Iran. A maimakon haka, da alama harin ya karfafa ikon hukumomin Iran bisa kara dankon hadin kai a tsakaninsu da mabambantan sassan siyasa da suke da sabanin ra’ayi, da rage damar yin sulhu da kuma karfafa muryoyin masu kishin kasa da ke kara yekuwar nuna wa al’ummar kasar cewa wannan yakin na gwagwarmayar dorewar kasar ne. Don haka, ake ganin bin hanyar diflomasiyya ta gaskiya tare da Amurka zai yi matukar wahala. Ana iya samun maslaha amma ta wucin-gadi, amma babu zancen amincewa da juna.

Wani abin damuwa da masana yankin suka nuna shi ne girman ramuwar gayyar da take biyo bayan hare-haren. Martanin Iran, wanda ya hada da harba makami mai linzami da tattaro kungiyoyin kawance a duk fadin yankin Gabas ta Tsakiya, ya nuna irin karfin da wasu manazarta ke ganin Amurka da Isra’ila suna masa kallon reni. Kuma wannan ne zai zama silar kara fadada rikicin Gabas ta Tsakiya wanda tuni ya shafi kasashe da dama, lamarin da ke kara nuna fargabar barkewar fadan da zai dade ana yi yankin. Sannan wadanda suka haddasa fitinar ba su da wata taswirar kawo karshen lamarin ko takamaimiyar hanyar siyasar da za a bi.

ADVERTISEMENT

Abubuwan da ke faruwa sun zarce batun matakin sojin da aka dauka. Masu sharhi na ganin lamarin yana da illoli ta fuskar diflomasiyya, musamman ga Isra’ila, wadda a yanzu ke fuskantar karin matsin lamba daga kasashen duniya tun daga kan kisan kiyashinta na Gaza. Ga bangaren Amurka kuma, lamarin zai iya haifar mata da tutsu daga abokan hulda da ke fargabar wargajewar tsarin samarwa a kasuwar makamashi ta duniya da kuma sauran hanyoyin kasuwancin yanki. Kazalika, daukar matakin soji zai iya zama na dogon lokaci wanda hakan zai kara karkatar da hankali da albarkatun Amurka daga wasu abubuwan da ta sa gaba a duniya, kamar cike gibin kasuwanci da sauran matsaloli na cikin gida.

Trump ya yi yakin neman zabensa da cewa ba zai tsunduma Amurka cikin yaki na dogon lokaci ba a wa’adinsa. Amma yanzu ya saba lamba, kuma har manyan ’yan siyasar Amurka masu goyon bayan kudurinsa na siyasa irin su Marjorie Taylor Greene, Thomas Massie, Rand Paul, Turker Carlson da sauransu sun yi Allah wadai da yakin na Iran.

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Kisan jagoran addini na Iran Ayatollah Khomeini wani babban kuskure ne a cikin wannan yakin saboda ba wai kai a matakin kasar Iran yake da tasiri ba, yana da dimbin mabiya wadanda za su iya sadaukar da rayukansu a sassan duniya daban-daban wajen neman daukar fansa. Kuma matukar zuciyar dan’adam take kashe a kan wani abu, to ba a san ranar samun mafita ba.

Kamar yadda Hausawa ke yawan fada, fitina bacci take, kuma Allah ya la’anci mai tayar da ita, muna fata wannan la’ana ta tsaya kan wadanda suka tayar ba tare da sauran al’ummar da ba-ta -ji-ba-ba-ta-gani ba. (Abdulrazaq Yahuza Jere)

 

Iran
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
Iran
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo
  • Sulaiman
    Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta
  • Sulaiman
    Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya
  • Sulaiman
    Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

MASU ALAKA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa
Daga Birnin Sin

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Next Post
Kafar CGTN Ta Fitar Da Rahoto Game Da Hasashen Ababen Mayar Da Hankali Yayin Manyan Taruka Biyu Na Sin

Kafar CGTN Ta Fitar Da Rahoto Game Da Hasashen Ababen Mayar Da Hankali Yayin Manyan Taruka Biyu Na Sin

LABARAI MASU NASABA

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

July 16, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

July 16, 2026
Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.