Amurka da Isra’ila sun kaddamar da hare-hare kan Iran ne bisa wai “wani matakin da ya dace don kawar da barazana.” Amma da yawa manazarta da suka san yankin Gabas ta Tsakiya da kuma musamman tarihin kasar Iran mai shekaru sama da 2000 da kafuwa, suna ganin cewa harin na iya zama kuskure ko batan lissafi, bisa tunanin yadda sakamakon da zai biyo baya na iya daukar tsawon shekaru ta fuskar zaman lafiya, matsin lambar diflomasiyya, da kuma kara hadarin matsalar tsaro.
Masu lura da al’amura sun lura cewa daya daga cikin manya-manyan kura-kurai shi ne tunanin cewa matakin soji zai raunana tsarin siyasar Iran. A maimakon haka, da alama harin ya karfafa ikon hukumomin Iran bisa kara dankon hadin kai a tsakaninsu da mabambantan sassan siyasa da suke da sabanin ra’ayi, da rage damar yin sulhu da kuma karfafa muryoyin masu kishin kasa da ke kara yekuwar nuna wa al’ummar kasar cewa wannan yakin na gwagwarmayar dorewar kasar ne. Don haka, ake ganin bin hanyar diflomasiyya ta gaskiya tare da Amurka zai yi matukar wahala. Ana iya samun maslaha amma ta wucin-gadi, amma babu zancen amincewa da juna.
Wani abin damuwa da masana yankin suka nuna shi ne girman ramuwar gayyar da take biyo bayan hare-haren. Martanin Iran, wanda ya hada da harba makami mai linzami da tattaro kungiyoyin kawance a duk fadin yankin Gabas ta Tsakiya, ya nuna irin karfin da wasu manazarta ke ganin Amurka da Isra’ila suna masa kallon reni. Kuma wannan ne zai zama silar kara fadada rikicin Gabas ta Tsakiya wanda tuni ya shafi kasashe da dama, lamarin da ke kara nuna fargabar barkewar fadan da zai dade ana yi yankin. Sannan wadanda suka haddasa fitinar ba su da wata taswirar kawo karshen lamarin ko takamaimiyar hanyar siyasar da za a bi.
Abubuwan da ke faruwa sun zarce batun matakin sojin da aka dauka. Masu sharhi na ganin lamarin yana da illoli ta fuskar diflomasiyya, musamman ga Isra’ila, wadda a yanzu ke fuskantar karin matsin lamba daga kasashen duniya tun daga kan kisan kiyashinta na Gaza. Ga bangaren Amurka kuma, lamarin zai iya haifar mata da tutsu daga abokan hulda da ke fargabar wargajewar tsarin samarwa a kasuwar makamashi ta duniya da kuma sauran hanyoyin kasuwancin yanki. Kazalika, daukar matakin soji zai iya zama na dogon lokaci wanda hakan zai kara karkatar da hankali da albarkatun Amurka daga wasu abubuwan da ta sa gaba a duniya, kamar cike gibin kasuwanci da sauran matsaloli na cikin gida.
Trump ya yi yakin neman zabensa da cewa ba zai tsunduma Amurka cikin yaki na dogon lokaci ba a wa’adinsa. Amma yanzu ya saba lamba, kuma har manyan ’yan siyasar Amurka masu goyon bayan kudurinsa na siyasa irin su Marjorie Taylor Greene, Thomas Massie, Rand Paul, Turker Carlson da sauransu sun yi Allah wadai da yakin na Iran.
Kisan jagoran addini na Iran Ayatollah Khomeini wani babban kuskure ne a cikin wannan yakin saboda ba wai kai a matakin kasar Iran yake da tasiri ba, yana da dimbin mabiya wadanda za su iya sadaukar da rayukansu a sassan duniya daban-daban wajen neman daukar fansa. Kuma matukar zuciyar dan’adam take kashe a kan wani abu, to ba a san ranar samun mafita ba.
Kamar yadda Hausawa ke yawan fada, fitina bacci take, kuma Allah ya la’anci mai tayar da ita, muna fata wannan la’ana ta tsaya kan wadanda suka tayar ba tare da sauran al’ummar da ba-ta -ji-ba-ba-ta-gani ba. (Abdulrazaq Yahuza Jere)















Discussion about this post