ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Harin Iran: Amurka Da Isra’ila Sun Bata Lissafi

by CGTN Hausa and Sulaiman
3 months ago
Iran

Amurka da Isra’ila sun kaddamar da hare-hare kan Iran ne bisa wai “wani matakin da ya dace don kawar da barazana.” Amma da yawa manazarta da suka san yankin Gabas ta Tsakiya da kuma musamman tarihin kasar Iran mai shekaru sama da 2000 da kafuwa, suna ganin cewa harin na iya zama kuskure ko batan lissafi, bisa tunanin yadda sakamakon da zai biyo baya na iya daukar tsawon shekaru ta fuskar zaman lafiya, matsin lambar diflomasiyya, da kuma kara hadarin matsalar tsaro.

Masu lura da al’amura sun lura cewa daya daga cikin manya-manyan kura-kurai shi ne tunanin cewa matakin soji zai raunana tsarin siyasar Iran. A maimakon haka, da alama harin ya karfafa ikon hukumomin Iran bisa kara dankon hadin kai a tsakaninsu da mabambantan sassan siyasa da suke da sabanin ra’ayi, da rage damar yin sulhu da kuma karfafa muryoyin masu kishin kasa da ke kara yekuwar nuna wa al’ummar kasar cewa wannan yakin na gwagwarmayar dorewar kasar ne. Don haka, ake ganin bin hanyar diflomasiyya ta gaskiya tare da Amurka zai yi matukar wahala. Ana iya samun maslaha amma ta wucin-gadi, amma babu zancen amincewa da juna.

Wani abin damuwa da masana yankin suka nuna shi ne girman ramuwar gayyar da take biyo bayan hare-haren. Martanin Iran, wanda ya hada da harba makami mai linzami da tattaro kungiyoyin kawance a duk fadin yankin Gabas ta Tsakiya, ya nuna irin karfin da wasu manazarta ke ganin Amurka da Isra’ila suna masa kallon reni. Kuma wannan ne zai zama silar kara fadada rikicin Gabas ta Tsakiya wanda tuni ya shafi kasashe da dama, lamarin da ke kara nuna fargabar barkewar fadan da zai dade ana yi yankin. Sannan wadanda suka haddasa fitinar ba su da wata taswirar kawo karshen lamarin ko takamaimiyar hanyar siyasar da za a bi.

ADVERTISEMENT

Abubuwan da ke faruwa sun zarce batun matakin sojin da aka dauka. Masu sharhi na ganin lamarin yana da illoli ta fuskar diflomasiyya, musamman ga Isra’ila, wadda a yanzu ke fuskantar karin matsin lamba daga kasashen duniya tun daga kan kisan kiyashinta na Gaza. Ga bangaren Amurka kuma, lamarin zai iya haifar mata da tutsu daga abokan hulda da ke fargabar wargajewar tsarin samarwa a kasuwar makamashi ta duniya da kuma sauran hanyoyin kasuwancin yanki. Kazalika, daukar matakin soji zai iya zama na dogon lokaci wanda hakan zai kara karkatar da hankali da albarkatun Amurka daga wasu abubuwan da ta sa gaba a duniya, kamar cike gibin kasuwanci da sauran matsaloli na cikin gida.

Trump ya yi yakin neman zabensa da cewa ba zai tsunduma Amurka cikin yaki na dogon lokaci ba a wa’adinsa. Amma yanzu ya saba lamba, kuma har manyan ’yan siyasar Amurka masu goyon bayan kudurinsa na siyasa irin su Marjorie Taylor Greene, Thomas Massie, Rand Paul, Turker Carlson da sauransu sun yi Allah wadai da yakin na Iran.

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Kisan jagoran addini na Iran Ayatollah Khomeini wani babban kuskure ne a cikin wannan yakin saboda ba wai kai a matakin kasar Iran yake da tasiri ba, yana da dimbin mabiya wadanda za su iya sadaukar da rayukansu a sassan duniya daban-daban wajen neman daukar fansa. Kuma matukar zuciyar dan’adam take kashe a kan wani abu, to ba a san ranar samun mafita ba.

Kamar yadda Hausawa ke yawan fada, fitina bacci take, kuma Allah ya la’anci mai tayar da ita, muna fata wannan la’ana ta tsaya kan wadanda suka tayar ba tare da sauran al’ummar da ba-ta -ji-ba-ba-ta-gani ba. (Abdulrazaq Yahuza Jere)

 

Iran
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya
Iran
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
  • Sulaiman
    Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
  • Sulaiman
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
  • Sulaiman
    Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

MASU ALAKA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
Daga Birnin Sin

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
Daga Birnin Sin

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos
Daga Birnin Sin

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Next Post
Kafar CGTN Ta Fitar Da Rahoto Game Da Hasashen Ababen Mayar Da Hankali Yayin Manyan Taruka Biyu Na Sin

Kafar CGTN Ta Fitar Da Rahoto Game Da Hasashen Ababen Mayar Da Hankali Yayin Manyan Taruka Biyu Na Sin

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.