ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hatsarin Mota Yayi Sanadiyar Mutuwar Mutum 5, Ya Jikkata 13 A Filato

by Abubakar Sulaiman
6 months ago

Aƙalla mutane biyar ne suka rasa rayukansu, yayin da wasu 13 suka jikkata sakamakon wani mummunan hatsarin mota da ya faru a shataletalen Zangzat a garin Langtang, cikin ƙaramar hukumar Langtang ta Arewa a Jihar Filato, a ranar Lahadi da safe.

Rahotanni sun nuna cewa hatsarin, wanda ya faru da misalin ƙarfe 3 na asuba, ya shafi wata babbar mota (traila) da ke ɗauke da ƴan kasuwa daga Shendam zuwa Jos, ta hanyar Langtang. Motar ta kife ne a kusa da shataletalen Zangzat, lamarin da ya janyo asarfrrxaar rayuka da jikkata mutane da dama.

  • Gwamnan Filato Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP
  • Jami’an Tsaro Sun Tarwatsa Ƙungiyar Da Ke Safarar Makamai Tare Da Kama Mutane 3 A Filato 

Shugaban ƙaramar hukumar Langtang ta Arewa, Hon. Pirfa Jingfa Tyem, ya bayyana matuƙar damuwarsa kan aukuwar hatsarin a cikin wata sanarwa da babban sakataren yaɗa labaransa, Kum Precious Yakubu, ta sanya wa hannu. Sanarwar ta ce rahotannin farko sun nuna cewa hatsarin ya shafi mota mai rijistar Jihar Filato mai lambar JJN 383 YZ.

ADVERTISEMENT

A cewar sanarwar, binciken farko ya nuna cewa gudun wuce gona da iri da kuma lodin fiye da ƙima ne suka haddasa hatsarin. Sanarwar ta kara da cewa mutane biyar sun mutu nan take, yayin da kusan mutane 13 suka samu raunuka mabambanta, kuma tuni aka garzaya da su Babban Asibitin Langtang domin samun kulawa.

Hon. Tyem ya mika sakon ta’aziyyarsa ga iyalan waɗanda suka rasu, tare da yi wa waɗanda suka jikkata fatan samun sauƙi cikin gaggawa. Ya kuma buƙaci Hukumar Kiyaye Haɗurra ta Kasa (FRSC) da ta ƙara ƙaimi wajen wayar da kan jama’a a kuma aiwatar da dokokin hanya, musamman a kasuwanni, tashoshin mota da manyan hanyoyi, yayin da ya gargaɗi direbobi da masu dakon kaya da su guji gudu da lodin fiye da ƙima domin kare rayuka.

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara
  • Abubakar Sulaiman
    Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026
  • Abubakar Sulaiman
    Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP
  • Abubakar Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Ta Gargaɗi Masu Ɓoye Gas Ɗin Girki

MASU ALAKA

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara
Tsaro

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

June 25, 2026
Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026
Manyan Labarai

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

June 25, 2026
An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano
Labarai

An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

June 25, 2026
Next Post
Shugaba Xi Jinping Ya Mika Sakon Jaje Ga Takwaransa Na Switzerland Bisa Afkuwar Bala’in Gobara

Shugaba Xi Jinping Ya Mika Sakon Jaje Ga Takwaransa Na Switzerland Bisa Afkuwar Bala’in Gobara

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

June 25, 2026
Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

June 25, 2026
An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

June 25, 2026
APC Ta Dage Yakin Zaben Shugaban Kasarta A Kano

An Dakatar Da Shugaban APC Na Kebbi Da Kwamishina Kan Zaɓen Cike Gurbin Zuru

June 25, 2026
Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

June 25, 2026
EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.