Tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, ya isa Babbar Kotun Jihar Kaduna domin ci gaba da sauraron ƙarar da ake yi tsakaninsa da ICPC.
Tun da farko kotun ta ɗage sauraron buƙatar belin da ya shigar zuwa ranar 14 ga Afrilu, yayin da ake ci gaba da bin diddigin shari’ar.
- El-Rufa’i Ya Kafa Tubalin Tsaro Da Ilimi A Jihar Kaduna – Jafaru Sani
- Masu Zargin Uba Sani Kan Bashin el-Rufa’i Sun Jahilci Aikin Majalisa – Barista Bello
Ana tuhumar El-Rufai ne da laifuka guda 10 da suka haɗa da karkatar da kadarorin gwamnati da kuma safarar kuɗaɗe ba bisa ƙa’ida ba.
ADVERTISEMENT
Ana sa ran ci gaba da sauraron ƙarar zai ƙara bayyana yadda shari’ar ke tafiya, yayin da ɓangarorin da ke shari’a ke ci gaba da gabatar da hujjoji a gaban kotu.














Discussion about this post