Tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, ya ja hankalin jama’a yayin da aka ji yana tattaunawa kan taron jam’iyyar APC mai zuwa, a lokacin da ya isa Babbar Kotun Jihar Kaduna domin ci gaba da shari’arsa.
Rahotanni sun nuna cewa El-Rufai, wanda ICPC ke tuhuma, an ji yana tambayar wani abokinsa ko gobe ne za a gudanar da taron jam’iyyar, alamar cewa har yanzu yana cikin harkokin siyasa duk da shari’ar da yake fuskanta.
- Kwankwaso Ya Ce Sun Amince Da Rabon Iko Kashi 60% – 40% Da ADC
- Hotuna: El-Rufai Ya Isa Kotu Domin Ci Gaba Da Sauraren Shari’arsa
An tsaurara matakan tsaro a harabar kotun, inda jami’an tsaro suka mamaye wurare masu muhimmanci domin tabbatar da zaman lafiya yayin zaman kotun.
Ana shari’ar El-Rufai tare da wani ɗan kasuwa mai suna Amadu Sule kan tuhume-tuhume da suka hada da cin yin amfani da muƙami, da damfara da kuma bayar da fifiko ba bisa ƙa’ida ba.
A baya, an gurfanar da shi a gaban kotun tarayya ƙarƙashin jagorancin mai shari’a Rilwan M. Aikawa kan tuhume-tuhume guda 10 da suka shafi karkatar da kadarorin gwamnati da kuma safarar kuɗaɗe, yayin da ake sa ran yanke hukunci kan belinsa a ranar 14 ga Afrilu, 2026.















Discussion about this post