Hukumar Kwastam ta Nijeriya (NCS) a ranar Alhamis, ta ce ta kama litar PMS 85,300 wanda aka fi sani da man fetur a jihar Ogun.
Da yake zantawa da manema labarai a Legas, mukaddashin jami’an hukumar ta Kwastam (CAC), Hussein Ejibunu, ya ce jami’ansu ne suka kama motar dauke da man a kan hanyar fasakwarin su zuwa kasar waje.
A cewarsa, jami’an rundunar sun kuma kama buhunan shinkafa ‘yar kasar waje da aka yi fasa kaurinsu guda 9,000.
ADVERTISEMENT
Ya kara bayyana cewa, rundunar ta kama kayayyakin da aka yi fasa-kwaurin su wanda jimillar kudin su ya kai Naira biliyan 1.021 a watan Nuwamba 2022.
-
Abubakar Abbahttps://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
-
Abubakar Abbahttps://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
-
Abubakar Abbahttps://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
-
Abubakar Abbahttps://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/














