ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 29, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hukuncin Kotu Na Barazana Ga Zaben 2027 —INEC

by Yusuf Shuaibu
2 months ago
INEC

Hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC), ta yi gargadin cewa sabbin hukuncin kotu da suka shafi jadawalin tsare-tsaren ayyukanta na zaben 2027 na iya kawo cikas ga shirye-shiryen zaben idan ba a gaggauta warware su ba kan lokaci.

Shugaban INEC, Farfesa Joash Amupitan, shi ya bayyana hakan a ranar Talata yayin taron hukumar karo na biyu tare da shugabannin jam’iyyun siyasa a Abuja.

Amupitan ya bayyana cewa hukumar ta riga ta shiya daukaka kara kan hukunci biyu na manyan kotun tarayya wanda suka kalubalanci wasu lokuta da ke cikin jadawalin INEC na zaben 2027.

ADVERTISEMENT

A cewarsa, duk da cewa hukumar tana girmama hukuncin kotuna, hukuncin yana tayar da tambayoyi ta shari’a game da iyakokin ikon INEC na tsarin mulki da na doka wajen tsarawa da daidaita ayyukan zabe.

Manyan kotunan tarayya da ke Abuja sun yanke manyan hukunci biyu da suka soke lokuta a cikin jadawalin zaben 2027 da INEC ta fitar.

LABARAI MASU NASABA

Mun Yi Ƙoƙarin Sasanta Iran Da Amurka A Lokacin Gasar Kofin Duniya – Infantino

Gwamna Sule Ya Halarci Ƙaddamar da Kamfanin Jinlide•Qiangyu New Energy, Ya Ƙara Jaddada Aniyar Jawo Masu Zuba Jari

Kotunan sun yanke hukunci cewa a daidai lokacin da tsarin mulki ya bai wa INEC izinin fitar da jadawalin zabe, ba za ta iya amfani da ka’idojin gudanarwa don gajartawa ko karawa kan lokutan da dokar zabe ta 2026 ta tabbatar wa jam’iyyun siyasa ba.

Amma Amupitan ya bayyana cewa a shari’ar da jam’iyyar matasa ta shigar a kotu mai lamba ta No. FHC/ABJ/CS/517/2026, da aka yanke hukunci a ranar 20 ga Mayu, 2026, kotu ta kalubalanci wasu lokuta da ke cikin jadawalin hukumar da tsarin ayyukanta na zaben 2027.

Ya kara da cewa a cikin wani hukunci na daban da aka yanke a ranar 26 ga Mayu, 2026, a shari’ar mai lamba No. FHC/ABJ/CS/720/2026, wanda jam’iyyar SDP ta kai karar INEC a kotun, kan kotu ta tabbatar da ikon hukumar na fitar da jadawalin zabe amma ta soke wasu lokuta da suka shafi zaban ‘yan takara da maye gurbin ‘yan takara.

Shugaban INEC ya jaddada cewa ayyukan da ke cikin jadawalin hukumar suna da alaka da juna a matsayin hanyoyin aiki da aka tsara don tabbatar da gudanar da zabe cikin tsari da gaskiya da nasara.

Ya ce a yayin da dokar zabe ta tsara jaddawali don wasu ayyukan zabe da wasu muhimman tsare-tsare da dama ba a bayyana su a cikin doka ba, amma dole ne a hada su cikin dukkanin jadawalin zabe.

Duk da kalubalen shari’a, shugaban INEC ya tabbatar wa jam’iyyun siyasa da jama’ar Nijeriya cewa hkumarsa na ci gaba da jajircewa wajen gudanar da zaben 2027 bisa ga dokokin kundin tsarin mulki da dokar zabe da duk wasu umarnin shari’a da suka inganta.

A yayin da yake magana, shugaban cibiyar hadakar jam’iyyu (IPAC), Dakta Yusuf Mamman Dantalle, ya ce cire tsarin zaben fitar da gwani kai tsaye daga tsarin zaben Nijeriya ya ba da gudummawa sosai ga rikice-rikice da tashin hankali da kalubalen gudanarwa da jam’iyyun siyasa suka fuskanta yayin zaben fitar da gwani da aka kammala kwanan nan.

INEC
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Manufofin Tattalin Arzikin Gwamnatin Tinubu Sun Lalata Rayukan Al’ummar Nijeriya —ADC
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Jadawalin INEC:Kotun Daukaka Kara Ta Kassara Fatan Jam’iyyu Da ‘Yan Siyasa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Tinubu Da Atiku Da Obi Na Ci Gaba Da Zafafa Neman Kuri’un Arewacin Nijeriya
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Zaben 2027:Tikitin Muslim-muslim Na Jam’iyyar APC Ya Sake Tayar Da Kura

MASU ALAKA

Mun Yi Ƙoƙarin Sasanta Iran Da Amurka A Lokacin Gasar Kofin Duniya – Infantino
Manyan Labarai

Mun Yi Ƙoƙarin Sasanta Iran Da Amurka A Lokacin Gasar Kofin Duniya – Infantino

July 29, 2026
Gwamna Sule Ya Halarci Ƙaddamar da Kamfanin Jinlide•Qiangyu New Energy, Ya Ƙara Jaddada Aniyar Jawo Masu Zuba Jari
Labarai

Gwamna Sule Ya Halarci Ƙaddamar da Kamfanin Jinlide•Qiangyu New Energy, Ya Ƙara Jaddada Aniyar Jawo Masu Zuba Jari

July 29, 2026
Sana’ar Ƙosai: Remi Tinubu Ta Yi Kira ga Burna Boy da Davido Su Taimaka wa Talakawa
Labarai

Ba Ma Fatan Wani Ɗan Nijeriya Ya Kwana da Yunwa — Remi Tinubu

July 29, 2026
Next Post
Real Madrid Ta Kammala Ɗaukar Bernardo Silva Daga Man City

Real Madrid Ta Kammala Ɗaukar Bernardo Silva Daga Man City

LABARAI MASU NASABA

Cinikin Salah Zuwa Besiktas Ya Rushe

Cinikin Salah Zuwa Besiktas Ya Rushe

July 29, 2026
Mun Yi Ƙoƙarin Sasanta Iran Da Amurka A Lokacin Gasar Kofin Duniya – Infantino

Mun Yi Ƙoƙarin Sasanta Iran Da Amurka A Lokacin Gasar Kofin Duniya – Infantino

July 29, 2026
Sin Ta Yi Martani Game Da Yiwuwar Kara Kudaden Da Amurka Ke Kashewa Da Nufin Dakile Tasirin Kasar Sin

Sin Ta Yi Martani Game Da Yiwuwar Kara Kudaden Da Amurka Ke Kashewa Da Nufin Dakile Tasirin Kasar Sin

July 29, 2026
Gwamna Sule Ya Halarci Ƙaddamar da Kamfanin Jinlide•Qiangyu New Energy, Ya Ƙara Jaddada Aniyar Jawo Masu Zuba Jari

Gwamna Sule Ya Halarci Ƙaddamar da Kamfanin Jinlide•Qiangyu New Energy, Ya Ƙara Jaddada Aniyar Jawo Masu Zuba Jari

July 29, 2026
Ma’aikatar Kasuwanci Ta Sin Ta Fitar Da Takarda Game Da Matsayin Sin Kan Abin Da Ake Kira “Samar Da Kayayyaki Fiye Da Kima”

Ma’aikatar Kasuwanci Ta Sin Ta Fitar Da Takarda Game Da Matsayin Sin Kan Abin Da Ake Kira “Samar Da Kayayyaki Fiye Da Kima”

July 29, 2026
Sana’ar Ƙosai: Remi Tinubu Ta Yi Kira ga Burna Boy da Davido Su Taimaka wa Talakawa

Ba Ma Fatan Wani Ɗan Nijeriya Ya Kwana da Yunwa — Remi Tinubu

July 29, 2026
Kotun Ɗaukaka Ƙara Ta Dakatar Da INEC Game Da Soke Rajistar ADC Da Wasu Jam’iyyu

Kotun Ɗaukaka Ƙara Ta Soke Umarnin Cire Rajistar ADC Da Wasu Jam’iyyu Huɗu

July 28, 2026
Kayayyaki Masu Fasahar AI Sun Zamo Sabbin Abubuwa Masu Tasiri A Cinikin Waje Na Kasar Sin

Kayayyaki Masu Fasahar AI Sun Zamo Sabbin Abubuwa Masu Tasiri A Cinikin Waje Na Kasar Sin

July 28, 2026
Ruwa

2027: Gwamnan Kaduna Ya Sanar Da Sabon Mataimakinsa A Zaɓen Gwamna

July 28, 2026
Xi Jinping Ya Yi Bayani Kan Ayyuka Masu Nasaba Da Sinawan Dake Ketare

Xi Jinping Ya Yi Bayani Kan Ayyuka Masu Nasaba Da Sinawan Dake Ketare

July 28, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.