Hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC), ta yi gargadin cewa sabbin hukuncin kotu da suka shafi jadawalin tsare-tsaren ayyukanta na zaben 2027 na iya kawo cikas ga shirye-shiryen zaben idan ba a gaggauta warware su ba kan lokaci.
Shugaban INEC, Farfesa Joash Amupitan, shi ya bayyana hakan a ranar Talata yayin taron hukumar karo na biyu tare da shugabannin jam’iyyun siyasa a Abuja.
Amupitan ya bayyana cewa hukumar ta riga ta shiya daukaka kara kan hukunci biyu na manyan kotun tarayya wanda suka kalubalanci wasu lokuta da ke cikin jadawalin INEC na zaben 2027.
A cewarsa, duk da cewa hukumar tana girmama hukuncin kotuna, hukuncin yana tayar da tambayoyi ta shari’a game da iyakokin ikon INEC na tsarin mulki da na doka wajen tsarawa da daidaita ayyukan zabe.
Manyan kotunan tarayya da ke Abuja sun yanke manyan hukunci biyu da suka soke lokuta a cikin jadawalin zaben 2027 da INEC ta fitar.
Kotunan sun yanke hukunci cewa a daidai lokacin da tsarin mulki ya bai wa INEC izinin fitar da jadawalin zabe, ba za ta iya amfani da ka’idojin gudanarwa don gajartawa ko karawa kan lokutan da dokar zabe ta 2026 ta tabbatar wa jam’iyyun siyasa ba.
Amma Amupitan ya bayyana cewa a shari’ar da jam’iyyar matasa ta shigar a kotu mai lamba ta No. FHC/ABJ/CS/517/2026, da aka yanke hukunci a ranar 20 ga Mayu, 2026, kotu ta kalubalanci wasu lokuta da ke cikin jadawalin hukumar da tsarin ayyukanta na zaben 2027.
Ya kara da cewa a cikin wani hukunci na daban da aka yanke a ranar 26 ga Mayu, 2026, a shari’ar mai lamba No. FHC/ABJ/CS/720/2026, wanda jam’iyyar SDP ta kai karar INEC a kotun, kan kotu ta tabbatar da ikon hukumar na fitar da jadawalin zabe amma ta soke wasu lokuta da suka shafi zaban ‘yan takara da maye gurbin ‘yan takara.
Shugaban INEC ya jaddada cewa ayyukan da ke cikin jadawalin hukumar suna da alaka da juna a matsayin hanyoyin aiki da aka tsara don tabbatar da gudanar da zabe cikin tsari da gaskiya da nasara.
Ya ce a yayin da dokar zabe ta tsara jaddawali don wasu ayyukan zabe da wasu muhimman tsare-tsare da dama ba a bayyana su a cikin doka ba, amma dole ne a hada su cikin dukkanin jadawalin zabe.
Duk da kalubalen shari’a, shugaban INEC ya tabbatar wa jam’iyyun siyasa da jama’ar Nijeriya cewa hkumarsa na ci gaba da jajircewa wajen gudanar da zaben 2027 bisa ga dokokin kundin tsarin mulki da dokar zabe da duk wasu umarnin shari’a da suka inganta.
A yayin da yake magana, shugaban cibiyar hadakar jam’iyyu (IPAC), Dakta Yusuf Mamman Dantalle, ya ce cire tsarin zaben fitar da gwani kai tsaye daga tsarin zaben Nijeriya ya ba da gudummawa sosai ga rikice-rikice da tashin hankali da kalubalen gudanarwa da jam’iyyun siyasa suka fuskanta yayin zaben fitar da gwani da aka kammala kwanan nan.














Discussion about this post