ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 12, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hukuncin Kotu Na Barazana Ga Zaben 2027 —INEC

by Yusuf Shuaibu
33 seconds ago
INEC

Hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC), ta yi gargadin cewa sabbin hukuncin kotu da suka shafi jadawalin tsare-tsaren ayyukanta na zaben 2027 na iya kawo cikas ga shirye-shiryen zaben idan ba a gaggauta warware su ba kan lokaci.

Shugaban INEC, Farfesa Joash Amupitan, shi ya bayyana hakan a ranar Talata yayin taron hukumar karo na biyu tare da shugabannin jam’iyyun siyasa a Abuja.

Amupitan ya bayyana cewa hukumar ta riga ta shiya daukaka kara kan hukunci biyu na manyan kotun tarayya wanda suka kalubalanci wasu lokuta da ke cikin jadawalin INEC na zaben 2027.

ADVERTISEMENT

A cewarsa, duk da cewa hukumar tana girmama hukuncin kotuna, hukuncin yana tayar da tambayoyi ta shari’a game da iyakokin ikon INEC na tsarin mulki da na doka wajen tsarawa da daidaita ayyukan zabe.

Manyan kotunan tarayya da ke Abuja sun yanke manyan hukunci biyu da suka soke lokuta a cikin jadawalin zaben 2027 da INEC ta fitar.

LABARAI MASU NASABA

Kotu Ta Ɗaure Mutane 5 Kan Tallafa Wa Boko Haram

Gwamnatin Tarayya Za Ta Dauki Sabbin Ƴansanda 50,000 Da Karin Sojoji — Tinubu

Kotunan sun yanke hukunci cewa a daidai lokacin da tsarin mulki ya bai wa INEC izinin fitar da jadawalin zabe, ba za ta iya amfani da ka’idojin gudanarwa don gajartawa ko karawa kan lokutan da dokar zabe ta 2026 ta tabbatar wa jam’iyyun siyasa ba.

Amma Amupitan ya bayyana cewa a shari’ar da jam’iyyar matasa ta shigar a kotu mai lamba ta No. FHC/ABJ/CS/517/2026, da aka yanke hukunci a ranar 20 ga Mayu, 2026, kotu ta kalubalanci wasu lokuta da ke cikin jadawalin hukumar da tsarin ayyukanta na zaben 2027.

Ya kara da cewa a cikin wani hukunci na daban da aka yanke a ranar 26 ga Mayu, 2026, a shari’ar mai lamba No. FHC/ABJ/CS/720/2026, wanda jam’iyyar SDP ta kai karar INEC a kotun, kan kotu ta tabbatar da ikon hukumar na fitar da jadawalin zabe amma ta soke wasu lokuta da suka shafi zaban ‘yan takara da maye gurbin ‘yan takara.

Shugaban INEC ya jaddada cewa ayyukan da ke cikin jadawalin hukumar suna da alaka da juna a matsayin hanyoyin aiki da aka tsara don tabbatar da gudanar da zabe cikin tsari da gaskiya da nasara.

Ya ce a yayin da dokar zabe ta tsara jaddawali don wasu ayyukan zabe da wasu muhimman tsare-tsare da dama ba a bayyana su a cikin doka ba, amma dole ne a hada su cikin dukkanin jadawalin zabe.

Duk da kalubalen shari’a, shugaban INEC ya tabbatar wa jam’iyyun siyasa da jama’ar Nijeriya cewa hkumarsa na ci gaba da jajircewa wajen gudanar da zaben 2027 bisa ga dokokin kundin tsarin mulki da dokar zabe da duk wasu umarnin shari’a da suka inganta.

A yayin da yake magana, shugaban cibiyar hadakar jam’iyyu (IPAC), Dakta Yusuf Mamman Dantalle, ya ce cire tsarin zaben fitar da gwani kai tsaye daga tsarin zaben Nijeriya ya ba da gudummawa sosai ga rikice-rikice da tashin hankali da kalubalen gudanarwa da jam’iyyun siyasa suka fuskanta yayin zaben fitar da gwani da aka kammala kwanan nan.

INEC
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Matsalar Tsaro Da Tsadar Kayan Noma Na Barazana Ga Samar Da Abinci A Daminar Bana
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Zaben Fitar Da Gwani Na APC: Tinubu Zai Shiga Tsakani Wajen Warware Rikicin Jam’iyyar
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027:Gwamnoni Na Fuskantar Turjiya Wajen Gwagwarmayar Kare Kujerunsu Da Kuma Samar Da Magadansu
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Masana Tattalin Arziki Sun Yi Watsi Da Rahoton NBS Kan Tattalin Arziki

MASU ALAKA

Kotu Ta Ɗaure Mutane 5 Kan Tallafa Wa Boko Haram
Labarai

Kotu Ta Ɗaure Mutane 5 Kan Tallafa Wa Boko Haram

June 12, 2026
Gwamnatin Tarayya Za Ta Dauki Sabbin Ƴansanda 50,000 Da Karin Sojoji — Tinubu
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Za Ta Dauki Sabbin Ƴansanda 50,000 Da Karin Sojoji — Tinubu

June 12, 2026
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 51, 876 Sun Mika Wuya A Arewa Maso Gabas
Labarai

Tinubu Ya Jinjina Wa Jami’an Tsaro Kan Jajircewarsu Wajen Kawo Karshen Ta’addanci

June 12, 2026

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

INEC Ta Shirya Gudanar Da Zaben Cike Gurbi A Jihar Kano

Hukuncin Kotu Na Barazana Ga Zaben 2027 —INEC

June 12, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Raba Buhunan Taki Kyauta Ga Manoma 20,160

Gwamnatin Tarayya Ta Raba Buhunan Taki Kyauta Ga Manoma 20,160

June 12, 2026
Jiya Aka Fara Gasar Cin Kofin Duniya

Jiya Aka Fara Gasar Cin Kofin Duniya

June 12, 2026
Kotu Ta Ɗaure Mutane 5 Kan Tallafa Wa Boko Haram

Kotu Ta Ɗaure Mutane 5 Kan Tallafa Wa Boko Haram

June 12, 2026
GORON JUMA’A

GORON JUMA’A

June 12, 2026
Falalar Neman Tsari Daga Sharrin Shaidan

Falalar Neman Tsari Daga Sharrin Shaidan

June 12, 2026
Gwamnatin Tarayya Za Ta Dauki Sabbin Ƴansanda 50,000 Da Karin Sojoji — Tinubu

Gwamnatin Tarayya Za Ta Dauki Sabbin Ƴansanda 50,000 Da Karin Sojoji — Tinubu

June 12, 2026
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 51, 876 Sun Mika Wuya A Arewa Maso Gabas

Tinubu Ya Jinjina Wa Jami’an Tsaro Kan Jajircewarsu Wajen Kawo Karshen Ta’addanci

June 12, 2026
INEC

June 12, 2026
Yayin Da Dangote Ya Bayyana A Ganawar Neman Aiki

Yayin Da Dangote Ya Bayyana A Ganawar Neman Aiki

June 12, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.