• English
  • Business News
Thursday, July 3, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ina Fatan Na Kammala Mulki Lafiya Na Koma Katsina – Buhari

by Sadiq
2 years ago
in Manyan Labarai
0
‘Yan Nijeriya Na Da Riko Da Addini, Amma Hakan Bai Hana Su Sata Da Zamba Ba – Buhari
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban kasa Muhammadu, Buhari ya ce zai yi amfani da sauran watanni hudun da suka rage masa a matsayin shugaban kasa don jajircewa kafin ya mika mulki.

Ya yi wannan alkawarin ne a ranar Litinin a Damaturu yayin da yake jawabi a fadar Sarkin Damaturu, Hashimi II El-Kanemi.

  • Xi Ya Jaddada Muhimmancin Karfafa Cikakkun Managartan Akidun Gudanar Da Jami’iyyar Kwaminis Ta Kasar Sin
  • An Tabbatar Da Bacewar Fasinjoji 31 Bayan Kai Hari Kan Jirgin Kasa A Jihar Edo

Da yake tsokaci kan harkae tsaro, Buhari ya bukaci ‘yan Nijeriya da su kara samun yakini duba da yadda jami’an tsaro ke samun nasarar yaki da ta’addanci a Nijeriya.

“A sauran watanni hudu da ya rage min a matsayina na shugaban kasa, zan ci gaba da dagewa kuma ina fatan na yi ritaya cikin kwanciyar hankali,” in ji shi.

Shugaban ya kuma bayyana cewa gwamnati ta dukufa wajen kare hakkin yaran Nijeriya kan samun ilimi musamman wadanda Boko Haram ta raba da gidajensu.

Labarai Masu Nasaba

Atiku, Obi, El-Rufai, Amaechi Da Wasu Sun Halarci Taron ADC Na jam’iyyar Haɗaka

Isra’ila Ta Amince Da Tsagaita Wuta Na Tsawon Kwana 60 Da Hamas – Trump

Ya ce, ”Mun sha fama da yawa a kasar nan, amma zan yi kira gare ku da ku dage da kuma tabbatar da cewa ba ku bari wani ya sake wargaza mu ba”.

Ya nuna jin dadinsa da dawowar zaman lafiya a Jihar Yobe da kuma Arewa maso Gabashin Nijeriya.

Ya danganta wannan zaman lafiya da hazakar gwamna Mai Mala Buni na Jihar Yobe da takwaransa na Jihar Borno, Farfesa Babagana Umara Zulum.

A cewar Buhari, shugabannin biyu, sun jajirce wajen sake gina makarantu, cibiyoyin lafiya da cibiyoyin da bata-gari suka lalata.

Idan dai za a iya tunawa Buhari a ‘yan kwanakin nan ya yi fatan kammala shugabancin kasar nan domin zai yi nisa da Abuja da kuma sha’anin mulki.

Ya kuma bayyana cewa zai koma jiharsa ta Katsina wadda ke kan iyaka da Jamhuriyar Chadi domin ci gaba da rayuwa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Boko HaramBornoBuhariDamaturuKatsinaMatsalar TsaroMulkiYobe
ShareTweetSendShare
Previous Post

Xi Ya Jaddada Muhimmancin Karfafa Cikakkun Managartan Akidun Gudanar Da Jami’iyyar Kwaminis Ta Kasar Sin

Next Post

Tsohon Gwamnan Adamawa, Bindow Ya Sauya Sheka Daga APC Zuwa PDP

Related

Atiku, Obi, El-Rufai, Amaechi Da Wasu Sun Halarci Taron ADC Na jam’iyyar Haɗaka
Manyan Labarai

Atiku, Obi, El-Rufai, Amaechi Da Wasu Sun Halarci Taron ADC Na jam’iyyar Haɗaka

14 hours ago
Isra’ila Ta Amince Da Tsagaita Wuta Na Tsawon Kwana 60 Da Hamas – Trump
Kasashen Ketare

Isra’ila Ta Amince Da Tsagaita Wuta Na Tsawon Kwana 60 Da Hamas – Trump

17 hours ago
Ba Zan Bar Jam’iyyar PDP Ba – Gwamna Muftwang
Manyan Labarai

Ba Zan Bar Jam’iyyar PDP Ba – Gwamna Muftwang

21 hours ago
David Mark Da Aregbesola Sun Zama Shugaba Da Sakataren Jam’iyyar ADC
Manyan Labarai

David Mark Da Aregbesola Sun Zama Shugaba Da Sakataren Jam’iyyar ADC

23 hours ago
Farfesa Haruna Musa Ya Lashe Zaɓen Shugabancin Jami’ar Bayero Ta Kano
Manyan Labarai

Farfesa Haruna Musa Ya Lashe Zaɓen Shugabancin Jami’ar Bayero Ta Kano

1 day ago
Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Ta’adda Yellow Danbokolo A Zamfara
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Ta’adda Yellow Danbokolo A Zamfara

2 days ago
Next Post
Tsohon Gwamnan Adamawa, Bindow Ya Sauya Sheka Daga APC Zuwa PDP

Tsohon Gwamnan Adamawa, Bindow Ya Sauya Sheka Daga APC Zuwa PDP

LABARAI MASU NASABA

Kayayyakin Sin Sun Kara Baiwa Masu Sayayya Na Kasa Da Kasa Damar Samun Zabi

Kayayyakin Sin Sun Kara Baiwa Masu Sayayya Na Kasa Da Kasa Damar Samun Zabi

July 2, 2025
Gwamnatin Kano Ta Haramta Shigo Ƙarafu Daga Arewa maso Gabas

Gwamnatin Kano Ta Haramta Shigo Ƙarafu Daga Arewa maso Gabas

July 2, 2025
Firaministan Sin Zai Halarci Taron Shugabannin Kasashen BRICS Na 17 A Brazil Da Kuma Ziyarar Aiki A Masar

Firaministan Sin Zai Halarci Taron Shugabannin Kasashen BRICS Na 17 A Brazil Da Kuma Ziyarar Aiki A Masar

July 2, 2025
Sin Na Ci Gaba Da Cika Alkawarin Bude Kasuwarta Ga Duniya

Sin Na Ci Gaba Da Cika Alkawarin Bude Kasuwarta Ga Duniya

July 2, 2025
Tinubu Ya Ƙaddamar Da Cibiyar Fasahar Da Aka Lalata Lokacin Zanga-Zanga A Kano

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Cibiyar Fasahar Da Aka Lalata Lokacin Zanga-Zanga A Kano

July 2, 2025
Zambiya Ta Kaddamar Da Tashar Samar Da Wutar Lantarki Ta Hasken Rana Mafi Girma

Zambiya Ta Kaddamar Da Tashar Samar Da Wutar Lantarki Ta Hasken Rana Mafi Girma

July 2, 2025
Abubakar Malami Ya Fice Daga APC, Ya Koma ADC

Abubakar Malami Ya Fice Daga APC, Ya Koma ADC

July 2, 2025
Yawan Kudin Shiga Da Sin Ta Samu A Fannin Sana’ar Manhaja A Watanni 5 Na Farko Na Bana Ya Wuce Yuan Triliyan 5.5

Yawan Kudin Shiga Da Sin Ta Samu A Fannin Sana’ar Manhaja A Watanni 5 Na Farko Na Bana Ya Wuce Yuan Triliyan 5.5

July 2, 2025
Rukunin Ƴan APC A Kano Sun Nemi A Rushe Jagorancin Jam’iyyar A Jihar

Rukunin Ƴan APC A Kano Sun Nemi A Rushe Jagorancin Jam’iyyar A Jihar

July 2, 2025
Xi Ya Bukaci Kungiyoyin Matasa Da Dalibai Su Zurfafa Gyare-Gyare Da Kirkire-Kirkire Don Samun Sabbin Nasarori

Xi Ya Bukaci Kungiyoyin Matasa Da Dalibai Su Zurfafa Gyare-Gyare Da Kirkire-Kirkire Don Samun Sabbin Nasarori

July 2, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.