Jakadan musamman na gwamnatin kasar Sin game da batun yankin Gabas na Tsakiya Zhai Jun, ya yi kira da a dakatar da bude wuta, a matsayin matakin shawo kan tashin hankalin da ya barke a yankin.
Zhai Jun, wanda ya yi kiran a jiya Lahadi, yayin tattaunawarsa da ministan ma’aikatar harkokin wajen kasar Saudiyya Faisal bin Farhan Al Saud, ya bayyana matukar damuwa game da matsanancin yanayin da ake ciki a yankin Gabas na Tsakiya. Yana mai jaddada cewa, ingiza matakan wanzar da zaman lafiya, da kawo karshen tashe-tashen hankula, za su taimakawa matuka wajen shawo kan mummunan yanayin da yankin ya fada.
A nasa tsokaci kuwa, Faisal bin Farhan Al Saud, cewa ya yi Saudiyya na sane da hadarin dake tattare da kara tsanantar rikicin, da tasirin fantsamarsa, don haka ne ma ta kara kai zuciya nesa. Ya kuma ce yana fatan Sin za ta ci gaba da taka rawar gani wajen ingiza matakan dakatar da bude wuta, da kandagarkin sake tabarbarewar yanayi a yankin.
Har ila yau a dai jiyan, Zhai Jun ya zanta da babban sakataren majalisar hadin gwiwar kasashen yankin Gulf, Jassim Mohammad Al Budaiwi. Yayin zantawar da suka yi, Zhai Jun ya ce Sin za ta kara zurfafa kwazonta, da aiki tare da majalisar hadin gwiwar kasashen yankin Gulf, domin ingiza matakan zaman lafiya, da dakatar da rikici, kana da mara baya ga matakan sassauta matsanancin halin da ake ciki. (Saminu Alhassan)















Discussion about this post