ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Darussa Daga Ramadan Na 16: Amfani Da Dama Kafin Ta Wuce

by Nuhu Ubale Ibrahim
4 months ago
Ramadan

A cikin watan Ramalana muna koyon darasi mai girma, watau amfani da dama kafin ta kuɓuce. Domin dama idan ta shuɗe, ba lallai ta dawo da irin yanayinta ba. Lokaci kamar gajimare ne, yana wucewa ba tare da tsayawa ba.

Allah Maɗaukaki Ya tuna mana da ƙimar lokaci a cikin ayoyin azumi, inda Ya ce a cikin Suratul Baƙara aya ta (184): “Waɗansu kwanaki ne ƙididdigaggu” Watau Ramalana ba wata ba ne mai dawwama; kwanaki ne kaɗan, masu ƙidaya, masu iyaka. Wannan kalma ta ‘ƙididdigaggu’ tana tunasar da mu cewa duk wata dama da Allah Ya ba mu tana da iyaka. Idan muka yi sakaci da ita, za ta shuɗe kamar ba ta taɓa zuwa ba.

  • Darussa Daga Ramadan Na 14: Yawaita Kyauta Da Ihsani A Ramalana
  • Darussa Daga Ramadan Na 13: Tsayuwar Dare

Ramalana yana koya mana yadda za mu daraja lokaci. Yana koya mana cewa yini guda na iya zama hanyar samun gafara, dare guda na iya zama sanadin tsira, kuma awa guda na iya sauya makomar rayuwa.

ADVERTISEMENT

Idan muka san cewa kwanakin Ramalana ƙalilan ne, za mu yi ƙoƙari mu cika su da alheri. Za mu nisanci ɓata lokaci a kan abin da ba ya amfanar da mu. Za mu fahimci cewa jinkiri da sakaci su ne manyan maƙiyan nasara.

Wannan darasi bai tsaya a kan Ramalana kaɗai ba. Rayuwarmu gaba ɗaya ‘kwanaki ne ƙididdigaggu’ Shekaru suna wucewa, ƙuruciya tana gushewa, ƙarfi yana raguwa. Duk wanda ya fahimci haka, to zai yi gaggawar cika rayuwarsa da ayyukan da za su amfane shi a duniya da Lahira.

LABARAI MASU NASABA

Menene Hukuncin Yin Aure Da Cikin Shege?

Matar Gwamnan Zamfara Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Tsarin Bunƙasa Ilimin Ƴa Mace

Ramalana wata dama ce ta sabunta rayuwa. Idan muka iya amfani da kwanakin nan yadda ya kamata, za su zama hujja a gare mu, ba hujja a kanmu ba. Saboda haka, mu riƙe kowace rana a matsayin baiwa a gare mu. Mu riƙe kowane dare a matsayin wata dama ce babba a tare da mu. Kada mu bari lokutanmu su tafi a iska. Domin idan dama ta wuce, ba za ta dawo da irin darajarta ba.

Allah Ya taimake mu wajen amfani da lokutanmu cikin abin da zai amfane mu, Ya sa kwanakinmu su zama masu albarka, Ya kuma ba mu kyakkyawan ƙarshe. Amin.

Ramadan
Nuhu Ubale Ibrahim
+ postsBio
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    Layya Babbar Ibada A Musulunci Na 1
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    Karamar Sallah: Sallar Idi A Wajen Musulmi…
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    SAHUR [Falalarsa Da Fa’idojinsa] Na 23
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    SAHUR [Falalarsa Da Fa’idojinsa] Na 22

MASU ALAKA

Yadda Jariri Ke Koyon Tsotsar Nonon Uwa Kafin Haihuwa
Fatawa

Menene Hukuncin Yin Aure Da Cikin Shege?

June 21, 2026
Matar Gwamnan Zamfara Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Tsarin Bunƙasa Ilimin Ƴa Mace
Ilimi

Matar Gwamnan Zamfara Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Tsarin Bunƙasa Ilimin Ƴa Mace

June 20, 2026
Hukumar Ilimin Bai-ɗaya Ta Jihar Yobe Ta Raba Kayan Karatu
Ilimi

Hukumar Ilimin Bai-ɗaya Ta Jihar Yobe Ta Raba Kayan Karatu

June 20, 2026
Next Post
An Yi Zama Na Biyu Na Taron Majalisar Wakilan Jama’ar Kasar Sin

An Yi Zama Na Biyu Na Taron Majalisar Wakilan Jama’ar Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

’Yansanda Sun Kama Mutane 57 Da Ake Zargi Da Ayyukan Ta’addanci A Adamawa

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.