Uwargidan Gwamnan Zamfara , Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta sha alwashin za ta ci gaba da taimakawa ilimin ƴaƴa mata a Jihar Zamfara.
Huriyya Dauda, wadda ta yi maganar hakan ne ta hannun mai,Sakatariyar ta da ke magana a madadin ta kan harkokin ƴan jaridu, Rabi Yusuf,a ranar Asabar.Ita ce ta fi kowa kan lamarin da ya shafi, ko yake da alaƙa da duk wani abinda ke da alaƙa da ci gaban da kuma kare ƴancin ƴa mace ta hanyar kare duk lamarin da yake da alaƙa da ci gaban ta da kuma wayar da kai domin hana yaɗuwar cin mutuncin da akan yi wa ,mata ta hanyar wayar da kan al’ummar musamman ma mata.
Ya kuma kamata ita kafar ta wayar da kan mata saboda kawar da duk wani lamarin da yake da alaƙa da tashin hankali da cin mutuncin mata, ko nuna masu lamarin da ya shafi nuna masu wariya ta hanya amafani da mata tun daga ƙauyuka, ana kuma yin hakan ne kai tsaye da Iyaye da kuma Shugabannin al’umma.
Bayanin ya ci gaba da bada labarin yadda ta sauya da kuma da mutanen karkara kan muhimmancin gyara kan lamarin da ya shafi ilimi a Jihar ta Zamfara domin tabbatar da cewar irin Shugabannin mata da za a samu na gaba, a Zamfara an shirya tsaf ta maganar horarwar da suka samu ta hanyar ilimi a makarantu, wanda hakan zai nuna cewar a shirye suke su yi wani jagoranci na al’umma.
A kan lamarin bunƙasa wa mata domin su tsaya da ƙafafun su,ta bayyana cewar “ a cikin shekarar 2025 kaɗai, Lfiye da mata 5,018 a faɗin Jihar ta Zamfara sun sanu horo na musamman kan harkokin kasuwanci, bayan haka kuma an taimaka masu da abubuwan da za su taimaka masu wajen duk wata harka ta kasuwanci da za su yi, wato kamar irin su harkokin ƙananan kasuwanci, yana rage fatara ga kua basu dama ta murya wadda za ta taimaka masu duk wajen harkokin da suka shafi ci gaban tattalin arzikin wuraren da suke zama.
“Lamarin na bunƙasar ci gaban tattalin arziki an ƙara samar ma shi wurin zama ne lokacin da aka yi wani tsari na bunƙasa tattalin arzikin na mata inda aka zabi, 500 daga sassa daban – daban na JIhar Zamfara inda suka zo aka kuma basu tallafin kuɗaɗe. Shi tasari ya yi matuƙar taimakawa wajen samar da hanyar da tafi dacewa wajen bunƙasa tattalin arzikin iyalai lokacin da tsarin tada komaɗar tattalin arziki na Shugaban ƙasa Tinubu ya fa yi wa al’umma bulalar shiga cikin halin ƙunci,ga babu kuɗi ga kuma tsadar rayuwar, wannan ya taimakawa masu ƙaramin ƙarfi inda ɗan ƙaramin kasuwancin da suke yi ya ƙara bunƙasa wanda sai kuma rayuwar su ta ƙara samun inganta.”
“Bugu da ƙari matar Gwamnan ba ta tsaya a anan bane, domin kuwa ta sake gabatar da wani tsari na bunƙasa mata da matasa da taimaka ma su ta sashen da ya shafi aikin gona. Ta shi tsarin kaɗai akwai fiye da mutane 300 da suka amfana, an samar masu da kayan aikin gona na zamani, ga kuma cikakkiyar horarwa, bugu da ƙari kuma ga kuɗaɗen da mutum zai fara duk irin bangaren noman da ya zaba dai, ga kuma wani tsarin da shi ma ba ƙaramar gudunmawa ya bayar ba wato irin wayar, da kan al’ummar da aka yi na yin lambun cikin gida,wannan, ma ya ƙarawa al’umma kayan abinci a sauƙaƙe kamar dai yadda bayanin ya nuna,”.
Akwai ma wani abu wanda yin hakan ya bada muhimmiyar gudunmawa ta yadda wani tsarin da ta bullo da shi,a gargajiyance wato yadda aka yi Firig na gargajiya ta hanyar amfani da kayan gargajiya ga kuma ƙungiyoyin mata da kuma Shugabannin al’umma, ko shakka babu tsarin na ta ya sa kowa ya gane da amfani ga al’umma, ya kuma san ba mantawa aka yi da shi ba, lokaci zuwa lokaci ana tuntubar juna, daga ƙarshe kuma sai maganar haɗin kai wadda ta maida su al’ummar Zamfarar suka kasance tsintsiya maɗaurinki ɗaya.















Discussion about this post