ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jami’in DSS Na Bogi Da Wasu Sun Shiga Hannu A Osun

by Sadiq
4 years ago
DSS

Rundunar ‘yansandan Jihar Osun ta sanar da kama wani jami’in DSS na bogi da wasu mutane bakwai da ake zargin masu garkuwa da mutane ne da wasu mutane uku bisa laifin fashi da makami.

Kakakin rundunar ‘yansandan, SP Yemisi Opalola, ta shaida wa manema labarai ranar Talata a Osogbo cewa, an kama wadanda ake zargin ne a wasu ayyuka da suka gudanar a jihar.

  • Sin Ta Bukaci Amurka Da Ta Kai Zuciya Nesa Game Da Batun Kumbon Farar Hula Da Ta Harbo
  • Masana’antun Kasar Sin Sun Taka Rawa Wajen Farfado Da Tattalin Arzikin Duniya

Opalola ta bayyana sunan wanda ake zargin jami’in bogi ne na hukumar DSS, Olaleye Oluseyi, mai shekaru 46.

ADVERTISEMENT

Ta ce wanda ake zargin yana karbar kudi daga hannun mutane ne bisa hujjar sama musu aiki a hukumar DSS.

Kakakin rundunar ta kara da cewa an kama Oluseyi ne a ranar 15 ga watan Janairu, biyo bayan rahoton sirri da aka samu cewa yana bayyana kansa a matsayin jami’in DSS yana yaudarar mutane.

LABARAI MASU NASABA

Direbobi 123 A Kano Suna Fuskantar Tuhuma Kan Laifin Keta Dokokin Amfani Da Lambar Mota

‘Yansanda Sun Kama Mutum Biyu Kan Zargin Damfarar Wayar Salula A Jihar Adamawa

“Ba tare da bata lokaci ba jami’an sa ido na rundunar ‘yansanda suka dauki mataki, suka kama wanda ake zargin, sannan ya amsa laifin damfarar wani Taiwo Victor kan kudi Naira 112,000, bisa nema masa aikin DSS.

“Lokacin da a kama shi, an kuma samu wata hular fuska dauke da rubutun hukumar kiyaye hadura ta tarayya a hannunsa.”

Opalola ta kuma ce an kama wata mata ‘yar shekara 23 da wasu mutane biyu da laifin hada baki da kuma aikata fashi da makami.

Ta ce biyu daga cikin wadanda ake zargin sun zo Osogbo ne daga Legas a ranar 28 ga watan Janairu, inda suka tare a wani otal tare da taimakon matar da ake zargin.

Kakakin ya kara da cewa mutanen ukun sun yi wa wadanda abin ya rutsa da su ne, inda suka yi wa daliban makarantar F

Kwalejin Fasaha ta Ede 20 fashi a gidajen kwanansu.

Ta ce za a gurfanar da dukkan wadanda ake zargin a gaban kotu bayan an kammala bincike.

MASU ALAKA

Direbobi 123 A Kano Suna Fuskantar Tuhuma Kan Laifin Keta Dokokin Amfani Da Lambar Mota
Kotu Da Ɗansanda

Direbobi 123 A Kano Suna Fuskantar Tuhuma Kan Laifin Keta Dokokin Amfani Da Lambar Mota

July 18, 2026
An Kama Matashi A Kano Kan Zargin Kashe Abokinsa
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Kama Mutum Biyu Kan Zargin Damfarar Wayar Salula A Jihar Adamawa

July 18, 2026
Disu
Kotu Da Ɗansanda

IGP Disu Ya Hana Jami’an Ƴansanda Yin Amfani Da TikTok Da Instagram Da Sauransu

June 26, 2026
Next Post
An Bukaci DSS Ta Yi Bincike Kan Kai Wa Ayarin Motocin Matar Gwamnan Adamawa Hari

An Bukaci DSS Ta Yi Bincike Kan Kai Wa Ayarin Motocin Matar Gwamnan Adamawa Hari

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

September 9, 2026
Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

September 9, 2026
Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

September 9, 2026
Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

September 9, 2026
Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

September 9, 2026
Bikin CIFTIS Zai Ingiza Bude Kofa A Kasar Sin

Bikin CIFTIS Zai Ingiza Bude Kofa A Kasar Sin

September 9, 2026
“Ajin Tashar Sararin Samaniya Na Hong Kong Da Macau” Ya Kara Wa Matasa Sha’awar Kimiyya Da Karfafa Kishin Kasa

“Ajin Tashar Sararin Samaniya Na Hong Kong Da Macau” Ya Kara Wa Matasa Sha’awar Kimiyya Da Karfafa Kishin Kasa

September 9, 2026
’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja

’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja

September 9, 2026
Taron Kolin Urumqi Ya Mayar Da Hankali Kan Kwarewar Shugabanci A Xinjiang Da Muhimmancinta Ga Duniya

Taron Kolin Urumqi Ya Mayar Da Hankali Kan Kwarewar Shugabanci A Xinjiang Da Muhimmancinta Ga Duniya

September 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.