ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

JIBWIS Ta Aurar Da Mahaddata Da Makaranta Ƙur’ani Mata Marayu 30

by Rabi'u Ali Indabawa and Sulaiman
7 months ago
JIBWIS

Kungiyar Jama’atu Izalatil Bid’a Wa’ikamatus Sunnah (JIBWIS), reshen Abuja ta gudanar da taron aurar da mata marayu mahaddata Ƙur’ani 10 da makaranta 20 ranar Laraba a Shalkwatar kungiyar dake Abuja.

 

Shugaban Kungiyar na Kasa, Sheikh Dr. Abdullahi Bala Lau, shi ya jagoranci ɗaurin auren. Da yake jawabi yayin gudanar da taron, Shehun malamin, ya ja hankalin al’ummar Musulmi kan muhimmacin kula da marayu da irin falal da ladan dake tattare da faranta wa marayu, inda ya ba da misali da yadda shugaban halitta Annabi Muhammad SAW, ya taso yana maraya cikin rashin uwa da uba, wanda ya ce Allah ya yi hakan ne domin mutane su sani cewa, kowa zai iya tsintar kansa a wannan matsayi.

ADVERTISEMENT
  • Yadda Fasahar Sin Ke Agaza Wa Samun Wadataccen Hatsi A Afirka
  • Yanzu- Yanzu An Sako Masu Ibadar da Aka Yi Garkuwa Da Su A Kaduna

Ya ce, “Manzon Allah (SAW) yana cewa duk wanda ya kula da maraya, to zai zauna kusa da ni a aljanna. Sannan a wani Nassin manzon Allah yana cewa, taimako da kuke samu duk Allah yana baku ne saboda tausaya wa masu raunin da suke cikinku.”

 

LABARAI MASU NASABA

’Yan Takarar ADC A Arewa Maso Yamma Sun Yi Alƙawarin Biyan N110,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

Na Sayar Da ’Ya’yana, Na Sace Wasu 19 – Wata Da Ake Zargi Da Safarar Yara

Sannan ya ce, Allah kadai shi ne ya san wane ne zai zama maraya. Sai ya bar mu da darasi da aya don mu tausaya wa maraya. Ya ja hankalin masu rike da marayu da su guji muzguna musu da cinye musu hakki.

 

A jawabin da ya yi ga manema labarai a yayin taron, mataimakin shugaban kwamitin marayu na kasa, sannan shugaban kwamitin marayu na kungiyar reshen Abuja, Abdullahi Abdulmalik Digi, cewa ya yi, wannan taro na aurar da mata marayu makaranta Alƙur’ani, akan yi shi ne sau daya a shekara, inda ake tattara marayu mata sannan a ɗauki nauyin aurar da su a ɓangarori biyu: na farko, waɗanda suka haddace Ƙur’ani, ɗaya ɓangaren kuma, waɗanda basu haddace ba.

 

Ana tantance mahaddata ne ta hanyar shirya Musabaka domin tabbatar da ingancin haddarsu, ba tare da la’akari da an san daga inda yarinya ta fito ko iyayenta ba, domin suna ba da cigiya ne sai a kawo su a tantance.

 

Maryam Hamza Imam, na ɗaya daga cikin marayu matan da aka aurar, ta bayyana wa LEADERSHIP Hausa irin farin cikinta da godiya ga wannan Kungiya ta JIBWIS da addu’ar Allah ya saka musu da alheri.

JIBWIS
Rabi'u Ali Indabawa
+ posts Bio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙungiya Ta Gudanar Da Zaɓen Sabbin Shugabanninta A Abuja
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Jihar Katsina Da UNICEF Sun Ceto Rayuwar Yara Ta Hanyar Samar Da Abinci Mai Gina Jiki
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Yadda Tinubu Ya Kashe Naira Biliyan 37.64 A Tafiye-tafiye
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ta’addaci: Mutum 14,500 Sun Bace A Arewa Maso Gabas
JIBWIS
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Na Sayar Da ’Ya’yana, Na Sace Wasu 19 – Wata Da Ake Zargi Da Safarar Yara
  • Sulaiman
    Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan
  • Sulaiman
    ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto
  • Sulaiman
    PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

MASU ALAKA

’Yan Takarar ADC A Arewa Maso Yamma Sun Yi Alƙawarin Biyan N110,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi
Manyan Labarai

’Yan Takarar ADC A Arewa Maso Yamma Sun Yi Alƙawarin Biyan N110,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

September 9, 2026
Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa
Labarai

Na Sayar Da ’Ya’yana, Na Sace Wasu 19 – Wata Da Ake Zargi Da Safarar Yara

September 9, 2026
Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila
Manyan Labarai

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
Next Post
Binciken CGTN: Gasar Wasannin Olympics Ta Hunturu Ta Milan-Cortina Ta 2026 Ta Kunna Haske Fiye Da Na Kankara Da Dusarta 

Binciken CGTN: Gasar Wasannin Olympics Ta Hunturu Ta Milan-Cortina Ta 2026 Ta Kunna Haske Fiye Da Na Kankara Da Dusarta 

LABARAI MASU NASABA

’Yan Takarar ADC A Arewa Maso Yamma Sun Yi Alƙawarin Biyan N110,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

’Yan Takarar ADC A Arewa Maso Yamma Sun Yi Alƙawarin Biyan N110,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

September 9, 2026
Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

Na Sayar Da ’Ya’yana, Na Sace Wasu 19 – Wata Da Ake Zargi Da Safarar Yara

September 9, 2026
Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.