Duba da irin daukin da Gidauniyar Dangote, ta fitaccen dan kasuwa kuma shugaban rukunin kamfanonin Dangote, Alhaji Aliko Dangote ke ci gaba da bayarwa a fannoni daban daban a jihar Kano, wasu daga cikin manyan shugabanni a bangren kasuwanci da wasu jigajigai a fannin kafafen yada labarai da ke a jihar, sun jijina wa fitaccen dan kasuwa Dangoteakan wannan daukin.
Wannan yabon na zuwa ne, biyo bayan rattaba hannun yarjejeniya, a tsakanin gidauniyar da kuma gwamnatin Kano musamman kan yadda Cibiyar bayar da horon koyon sana’oin hannun na dogaro da kai ta Aliko dangote, ta shafe shekaru ta na samar da dauki, kan koyon sana’oin hannun na dogaro da kai.

Kazalika, gidauniyar wacce aka zuba miliyoyin Naira a cikin ta, kuma a yanzu ta ke a yankin Ganaja na jihar Kogi, tuni aka kammala ta ana kuma kan gudanar da shirye- shiryen m, kaddamar da ita.A jawabinsa a wajen rabbata hannun yarjejeniyar, shugaban kungiyar kula da masana’antu ta kasa na shiyoyin Kano da Jigawa wato MAN Muhammad Bello Isyaku Umar, ya yi nuni da cewa, Cibiyar, ta kasance daga cikin wacce za ta taimaka wajen rage zaman kashe Wando, a daukacin fadin kasar, musamman a tsakanin matasa. Ya kara da cewa, Cibiyar kamar irin wannan ta Aliko Dangoteshirye-shiyen da take gudanawa, za su taimaka wa, musamman matasan da ke a jihar, wajen samun kwarewar koyon sana’oin hannun na dabarun zamani.Ya ci gaba cewa, za a amfana da cibiyar, musamman a bangaren kula da kiwon lafiya, bayar da horon koyon sana’oin a tsakanin mata, samar da ilimin Boko, samar da ruwan sha, rage talunci da sauransu.
A cewarsa, wannan daukin, zai kasance tamkar, tallafawa irin kokarin dagwamnatin Kano ke ci gaba da yi ne, na inganta rayuwar Kanawa, musamman marasa karfi.
Shi kuwa a na sa jawabin kwararen danjarida kuma Manajan gidan Radiyo mallakar gwamnatin jihar Abubakar Adamu, ya ce, wannan daukin, zai jima ana ganin alfanunsa a jihar musamman duba da cewa, a Kano, akwai dimbin matasan da gwamnatin jihar kawai, ba za ta iya samar masu da ayyukan yi ba.

Ya yi nuni da cewa, babban mahimmancin da wannan daukin ya ke da shi shi ne, ba wai kawai ya karyata, bangare daya ba ne, amma abu ne, da hada da kula da kiwon lafiya, samar da abinci mai gina jiki, ilimin Boko, samar da kowon sana’oin hannun a tsakanin mata, bunkasa rayuwar alumomi da sauransu.














