Shugaban hukumar kula da Tashoshin Jiragen Ruwa ta Ƙasa NPA, Dakta Abubakar Ɗantsoho, ya bayyana cewa, NPA ta samu sahalewar dala biliyan ɗaya domin gudanar da shirin zamantar da a tashoshin Jiragen Ruwan ƙasa
Ɗantsoho ya sanar da cewa, za a fara gudanar da aikin ne, kafin a zango na uku na shekarar 2026.
Shugaban ya ƙara da cewa, shirn na zamantar da tashoshin, wanda wata babbar nasara ce, wanda kuma gwamnatin tarayya ta ƙaddamar na ɗaya daga cikin shirin da ke a ƙarƙashin ma’aiakatar bunƙasa tattalin arziki na Teku
Ya ci gaba da cewa, an tsara shirin ne, bisa nufin, yi wa kayan aikin da ke a tashoshin Jiragen Ruwan ƙasar, garanbawul, musamman domin a ƙara ƙarfafa ayyukansu da ƙara tabatar da yin gasar hada-hadar kasuwanci a nahiyar Afirka.
Shugaban ya bayyana cewa, tuni aka kammala tsare-tsaren yadda za a gudanar da aikin tare da wasu daga ƙasar waje, wanda kuma fara aikin, ya haɗa da masu ruwa da tsaki abokan tuntuɓa da kuma sauran alumomin da ke a yankunan da tashoshin Jiragen Ruwan ƙasa.
A cewar Dakta Ɗantsoho, an riga an samu sahalewar gaba ɗaya, ta dala biliyan ɗaya, domin fara gudanar da aikin, tare da wasu abokan haɗaka da sauran hukumi na ƙasar waje.
“Mun riga mun kammala dukkan ƙa’idojin samar da kuɗin aikin, inda kuma ake sa ran za a fara gudanar da aikin ne, kafin a zango na uku na shekarar 2026,” inji Dakta Ɗantsoho.
Kazalika, shugaban hukumar ta NPA, ya bai wa ƴan Nijeriya tabbacin cewa, za su fara gani a ƙas, na kayan da za a samar domin gudanar da aikin sabunta tashoshin Jiragen Ruwan ƙasa.
Ya ƙara da cewa, za su fara ganin hakan ne, tun a zango na huɗu na shekarar 2026, inda ya yi nuni da cewa, shirin na zamantar da tashoshin, ana sa ran zai ƙara taimaka wa, wajen ƙara inganta ayyukan dsa ake gudnarwa a tashoshin.
“Shirin na zamantar da kayan da ake gudanar da ayyuakan a tashoshin Jiragen Ruwan, an tsara shi ne, bisa nufin yiwa kayan garanbawul, musamman domin su tafi kafaɗa da kafaɗa da sauran kayan aikin irin na faɗin duniya, “a cewar shugaban.
“A zahirance kuma a hukumance aikin na dala biliyan ɗaya, za a fara yinsa ne a zango na uku na shekarar 2026. Inji Ɗantsoho.
Ya ƙara da cewa, ƴan Nijeriya za su fara ganin aikin ne tare da samar da kayan aikin na zamani daga zango na huɗu na shekarar 2026.
Ya ci gaba da cewa, da zarar an kamala aikin zai rage ƙalubalen da ake fuskanta kusan na kaso hamsin a cikin ɗari, musamman na Jiragen ruwa da ake samu a tashoshin Jiragen Ruwan ƙasar tare da kuma ƙara inganta gudanar da ayyuka, a cikin sauƙi.
A cewar Ɗantsoho, aikin ba wai na ƙananan ma’aikata ba ne, aiki ne da ya haɗada, samar da kayan aikin na fasahar zamani, musamman kayan fasahar kimmiyar na ƁTS, da su ƙara taimaka wa, wajen zirga-zirgar Jiragen Ruwa da kuma gudanar da ayyuka a tashoshin, a cikin sauƙi.
“A yanzu kan ƙoƙarin tsara zirga-zirgar wasu Jiragen da a turance ake kira da tugboats da kuma wasu ƙananan Kwale-Kwale da kuma kan gyran Katangun kankaren Siminti da ke a Tashoshin Tin-Can da Apapa,” a cewar shugaban.
“Sanya kayan fasahar kimmiyar ta ƁTS, za ta taimaka matuƙa wajen da damar ci gaba da sanya Ido da kuma bayar da kariya ga ɗaukacin sararin Ruwan,” ini Ɗantsoho.
Shugaban ya ƙara da cewa, faɗaɗa guraren da ake ajiye kayan da aka tantancewa a Tashoshin kafin a fitar da su zuwa ƙetare wato EPT da kuma ƙara haɓaka ayyukan yin hada-hadar kasuwanci a tashoshin, na ɗaya daga cikin dabarun da za su ƙara matuƙar taimaka wa, wajen ƙara tara kuɗaɗen shiga, da kuma ƙara bunƙasa tattalin arzikin ƙasar.
Ɗantsoho ya sanar da cewa, NPA na ci gaba da bayar da fifiko, wajen ƙara ƙarfafa hada-hadar kasuwanci a tashoshin ƙasar, ƙara inganta ayyuka a tashoshin, tare da turawa gwamnatin tarayya kuɗaɗen shiga, ta hanyar sauye-sauyen da aka samar na yin amfani da fasahar zamani.
“Abinda muka bayar da fifiko akai shi ne, ƙara haɓaka hada-hadar kasuwanci a tashoshin, wanda hakan ya bai wa ƙasar, a zangon farko na shekarar 2026 kacal, damar samun rarar da ta kai ta Naira tiriliyan 7.54,” a cewar Ɗantsho.
Ɗantsoho ya bai wa masu ruwa da tsaki a fannin, tabbacin cewa, NPA za ta ci gaba da ƙara ƙaimi, wajen tara kuɗaɗen shiga wanda ake turawa a cikin gidaniyar tara kuɗaɗe ta CRF, tare da kuma ƙara inganta tsarin.
“Nan da sama da watanni sha biyu masu zuwa, masu ruwa da tsaki a fannin ina mai ba su tabbacin cewa, NPA za ta ci gaba da ƙara ƙaimi, wajen tara kuɗaɗen shiga wanda ake turawa a cikin gidaniyar tara kuɗaɗe ta CRF, tare da kuma ƙara inganta tsarin,” inji shugaban’
Haka zalika ya ce, NPA za ta ƙara ɗaga daragar kayan aikinta a sauran tashoshin Jiregen, domin a ƙara haɓaka ayyukansu.
“Za mu ƙara ɗaga daragar kayan aikinta a sauran tashoshin Jiregen, domin a ƙara haɓaka ayyukansu cikinsu har na Onne da Kalaba da kuma Warri,” a cewarsa .
Shugaban ya kuma sanar da cewa, aikin faɗaɗa EPT, zai bayar da gagarumar gudunmawa, wajen ƙara fitar da kayan da basu shafi fannin Mai ba, zuwa ƙetare, tare da bunƙasa shirin haɓaka tattalin arzki na gwamnatin tarayya..
Ya ce, NPA na kuma kan samar da tsarin PCS, wanda zai ƙara taimaka wa shirin NSW na ƙasa, musamman wajen rage cunkosn Jiragen Ruwa a tashoshin.
“Burin mu shi ne, muga a cikin sa’io 48 duk wani cunkoso an kawar da shi, a cikin tashoshin, wanda hakan zai ƙara bayar da damar gudanar da gasa ga hada-hadar kasunwanci a tashoshin, “inji Ɗ Dantsoho .














