ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kada Ku Yi Wa Tinubu Hukunci Da Abin Da Ya Aikata Shekaru 33 Da Suka Wuce — Buratai

by Abubakar Sulaiman
3 weeks ago

Tsohon Babban Hafsan Sojin Ƙasa, Laftanar Janar Tukur Buratai (mai ritaya), ya roƙi ƴan Nijeriya da kada su yi wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu kuɗin-goro da zargin ayyukan da suka auku shekaru 33 da suka gabata.

Ya bayyana hakan ne a daidai lokacin da ake yunƙurin sakin wasu takardu da ake zargin suna da alaƙa da binciken fataucin miyagun ƙwayoyi da ya shafi shugaban ƙasar, lamarin da Buratai ya ce bai kamata a bar shi ya bata sunan Nijeriya a idon duniya ba.

A cikin wata takarda da ya wallafa a shafinsa na Facebook a ranar Lahadi mai taken “Nijeriya a Gaba,” ya jaddada cewa wannan batu ya wuce shugaban ƙasa a matsayinsa na mutum ɗaya, domin lamari ne da ya shafi kimar ƴan Nijeriya miliyan 250 da kuma tattalin arzikin ƙasar. Idan ba a manta ba, wata kotu a Amurka ta ba wa Tinubu, FBI, da Ma’aikatar Shari’a wa’adin zuwa 28 ga watan Agustan 2026 don gabatar da dalilansu kan hana sakin wadannan takardu.

ADVERTISEMENT

Buratai ya nuna takaicinsa kan yadda za a bari wata kotun ƙasar waje ta yanke hukunci kan halayyar shugaban da ƴan Nijeriya miliyan da dama suka zaɓa, inda ya ce hakan zai iya zama tamkar katsalandan cikin harkokin siyasar Nijeriya, musamman idan aka yi la’akari da zaben 2027 da ke tafe.

Tsohon hafsan sojan ya tambayi ko akwai wani dan Najeriya da zai ce shi ne mutumin da yake a shekaru 33 da suka wuce, inda ya kara da cewa kamata ya yi a duba irin gudunmawar da Tinubu ya bayar, tun daga lokacin da ya zama gwamnan jihar Legas har zuwa shigarsa siyasar kasa.

LABARAI MASU NASABA

Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

Ya yi kira ga gwamnatin tarayya da ta warware matsalar ta fuskar diflomasiyya, tare da roƙon lauyoyin shugaban ƙasa da su dage wajen kare a saki wadannan takardu domin kiyaye mutuncin ofishin shugaban ƙasa da kuma martabar Nijeriya.

Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Iyalin El-Rufai Sun Bai Ministan Tsaro Wa’adin Kwana 7 Kan Zargin Rikicin Kudancin Kaduna
  • Abubakar Sulaiman
    Atiku Ya Zargi Gwamnatin Tarayya Da Cin Bashi Kamar Mashayin Da Kuɗi Ya Ƙarewa
  • Abubakar Sulaiman
    Boko Haram Ta Kai Hari Adamawa, Ana Fargabar Mutuwar Mutane 11
  • Abubakar Sulaiman
    Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Sokoto, Sun Kashe Mutane 7, Sun Yi Garkuwa Da 12

MASU ALAKA

Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara
Labarai

Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

September 10, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia
Manyan Labarai

Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

September 10, 2026
’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya
Labarai

’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

September 10, 2026
Next Post
An Kafa Tawagar Sin Da Za Ta Halarci Gasar Nuna Kwarewa Ta Duniya Ta 48

An Kafa Tawagar Sin Da Za Ta Halarci Gasar Nuna Kwarewa Ta Duniya Ta 48

LABARAI MASU NASABA

Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

September 10, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

September 10, 2026
’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

September 10, 2026
2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

September 10, 2026
Zabe: Gwamnatin Kano Ta Taƙaita Zirga-zirgar Mutane Da Ababen Hawa

Gwamna Yusuf Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Gano Waɗanda Suka Kashe Danshagamu

September 10, 2026
Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

September 9, 2026
Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

September 9, 2026
Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

September 9, 2026
Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

September 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.