ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kamfanin Mercedes Zai Shigar Da Osimhen Kara Kan Rashin Biyan Bashi

by Abba Ibrahim Wada
1 month ago
Mercedes

An ruwaito cewa kamfanin kera motoci na kasar Jamus Mercedes-Benz ya shigar da dan wasan tawagar Nijeriya da Galatasaray Bictor Osimhen kara a gaban wata kotu dake kasar Italiya kan zargin rashin kammala biyan kudin wata motar da ya saya a lokacin zamansa a kungiyar kwallon kafa ta Napoli.

A halin yanzu Osimhen yana daya daga cikin ‘yan wasan gaba mafi kwarewa a kwallon kafa a Duniya, ya taka leda a manyan kasashen Turai da suka hada da Belgium, Faransa, Italiya, da kuma Turkiyya, duk da haka, manyan nasarorin da ya samu sun zo ne a lokacin da ya lashe gasar Serie A ta kasar Italiya da kuma gasar Süper Lig ta kasar Turkiyya, inda ya lashe gasar tare da kungiyoyin Napoli da Galatasaray, bi da bi.

A lokacin zamansa na shekaru hudu da Napoli, Osimhen ya jagoranci kungiyar wajen lashe gasar Scudetto a karon farko cikin kusan shekaru 40, saboda wadannan nasarorin, komawarsa Galatasaray a bazarar da ta gabata ya sa ya zamo dan wasan da ya fi kowane dan wasan karbar albashi a tarihin gasar ta kasar Turkiyya da ake kira Turkish Süper Lig.

ADVERTISEMENT

Tauraron Super Eagles din a halin yanzu yana samun Yuro miliyan 20 a kowace shekara a matsayin albashi a Galatasaray, Osimhen ya samu yabo saboda ayyukansa na taimakon jama’a, yana yawan tallafa wa iyali, abokai, har ma da wadanda bai sani ba a shafukan sada zumunta, a karshen makon da ya gabata, ya dauki nauyin wasu magoya bayan Nijeriya domin su halarci wasan da Galatasaray ta doke kungiyar Fenerbahce da ci 3-0.

A cewar wani rahoto da jaridar Napolista ta fitar, Mercedes-Benz ta sanar da hukumomin Italiya game da bashin da take bin Osimhen, kamfanin ya yi ikirarin cewa Osimhen ya gaza kammala biyan kudin da ya sayi wata mota a shekarar 2023 kuma ya ki ya dawo da motar bayan ya kasa biya, sakamakon haka, ana zargin cewa dan wasan gaban mai shekaru 27 ya tara bashin Yuro 90,000 (kimanin Naira miliyan 142), wannan lamari ya bai wa mutane da dama mamaki ganin cewa albashin Osimhen na mako-mako ya zarce wannan adadin tun lokacin da ya lashe gasar Serie A.

LABARAI MASU NASABA

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Galatasaray Ta Sanya Farashin Yuro Miliyan 150 Kan Osimhen, Chelsea Ta Nuna Sha’awar Ɗaukarsa

Kwanan nan ya nuna tarin motocin dake cikin garejinsa wanda ya kunshi Lamborghini biyu, Rolls-Royce, da Mercedes-Benz—wadda watakila ita ce wadda ake magana a kai, zuwa yanzu dai wakilan Osimhen ba su fitar da wata sanarwa a hukumance ba, watakila dan wasan zai nemi warware matsalar da sauri domin ya mayar da hankali wajen taimaka wa kungiyarsa lashe kofin Super Lig na bana.

Mercedes
Abba Ibrahim Wada
Website |  + postsBio
  • Abba Ibrahim Wada
    Ko Kasan ‘Yanwasan Da Za Su Buga Kofin Duniya Na Ƙarshe?
  • Abba Ibrahim Wada
    Nijeriya Ta Samu Lambobin Yabo 16 A Wasannin Tseren Keke
  • Abba Ibrahim Wada
    Nijeriya Za Ta Karbi Bakuncin Babban Taron Hukumar CAF Na Bana
  • Abba Ibrahim Wada
    Shin Ko Arsenal Za Ta Mamaye Duniya?

MASU ALAKA

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya
Wasanni

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Galatasaray Ta Sanya Farashin Yuro Miliyan 150 Kan Osimhen, Chelsea Ta Nuna Sha’awar Ɗaukarsa
Wasanni

Galatasaray Ta Sanya Farashin Yuro Miliyan 150 Kan Osimhen, Chelsea Ta Nuna Sha’awar Ɗaukarsa

June 2, 2026
Super Eagles Ta Tafi Poland Domin Wasan Sada Zumunta
Adabi

Super Eagles Ta Tafi Poland Domin Wasan Sada Zumunta

May 31, 2026
Next Post
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

ADC: Kwankwaso Ya Musanta Jita-jitar Ficewa Daga Jam’iyyar, "Har Yanzu Bai Yanke Hukunci Ba"

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.