Gwamnatin Jihar Kano, ta hannun Rundunar Hadin Gwiwa ta Hukumomi da dama kan Dakile Shaye-Shayen Miyagun Kwayoyi, ta kaddamar da shirin shekara guda na gyaran rayuwar matasa 10,000 da ke da hannu wajen shaye-shayen miyagun kwayoyi, safarar kwayoyi da ayyukan kungiyoyin daba, tare da koyar da su sana’o’in dogaro da kai.
Shugaban rundunar, Muhuyi Magaji, ne ya bayyana hakan yayin wani taron manema labarai a Kano, inda ya ce an tsara shirin ne domin yaki da matsalar shaye-shayen miyagun kwayoyi da tashe-tashen hankula na kungiyoyin daba, tare da taimaka wa matasan da lamarin ya shafa su koma rayuwa mai amfani.
Magaji ya ce wadanda za su amfana da shirin za su fara samun kulawar lafiya da tsaftace jikinsu daga illar kwayoyi, da gyaran dabi’u da tunani, sannan a ba su shawarwari kan sana’a kafin a fara koyar da su sana’o’in dogaro da kai.
Ya ce, “Burinmu shi ne mu gyara rayuwar matasa 10,000 masu ta’ammuli da miyagun kwayoyi cikin shekara guda. Ba wai kawai za mu tura su gidan yari ko cibiyoyin gyaran hali ba ne.”
Ya bayyana cewa rundunar za ta farfado da cibiyoyin koyar da sana’o’i a fadin jihar, ciki har da cibiyar sarrafa fata da ke Sharada, da cibiyoyin dinki da samar da tufafi da ke Kura, Madobi, Dawakin Tofa, Danbatta, Gwarzo, Gezawa, Minjibir, Warawa da Dala.














