• English
  • Business News
Saturday, July 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Karuwar Nuna Wariya Alama Ce Ta Koma Bayan Kare Hakkin Bil Adama

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Karuwar Nuna Wariya Alama Ce Ta Koma Bayan Kare Hakkin Bil Adama

People hold signs saying "Say Their Names" and pay tribute to George Floyd and other Black lives lost to police brutality on the three-year anniversary of George Floyd's death at the Say Their Names Cemetery, Thursday, May 25, 2023, in Minneapolis. The murder of Floyd at the hands of Minneapolis police, and the fervent protests that erupted around the world in response, looked to many observers like the catalyst needed for a nationwide reckoning on racism in policing. (AP Photo/Abbie Parr)

Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Batun kare hakkin bil adama tsakanin manyan kasashe masu karfin fada aji, na cikin muhimman batutuwa dake jan hankali masharhanta a sassan duniya daban daban.

Ko shakka ba bu, ba wata alumma da ba ta fatan samun cikakkiyar kariya a fannonin hakkin bil adama daban daban, musamman a wannan lokaci da duniya ke samun ci gaba, da dunkulewa, ake kuma burin ganin dan adam ya yi rayuwa mai yalwa da walwala.

  • Sin Ta Yi Kira Da A Goyi Bayan CAR A Yunkurinta Na Shimfida Zaman Lafiya

To sai dai kuma wani abun lura a nan shi ne, yadda alummu daban daban ke kallon maanar kare hakkin bil adama, inda yayin da wasu ke kallon batun a matsayin wata manufa samar da ci gaba, da walwala, da gina alummar dan adam mai kyakkyawar makoma, wasu kuwa na amfani da batun kare hakkin bil adama ne a matsayin hanyar cin gajiyar siyasa, da nuna cewa su ne mafiya kwarewa a wannan fage.

Ga misali, a nan kasar Sin, akidar kare hakkin bil adama na nufin kare rayuka da walwalar alumma, da wanzar da zaman lafiya da ci gaban zamantakewar daukacin alummar kasa, da zamanantar da kasa daga dukkanin fannoni.

Kuma Sin ta amince cewa ba wata hanya dala tilo da za a ce ita ce kadai wadda bil adama zai bi wajen tabbatar da kare hakkokin bil adama, illa dai kawai ko wace kasa, ko yanki ya yi amfani da yanayin da yake ciki, wajen cimma nasarar kare hakkin alummar sa.

Labarai Masu Nasaba

Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa

Kasar Sin Na Da Muradin Zurfafa Hadin Gwiwar BRI Da Masar 

A daya bangaren kuwa, kasashen yamma, musamman Amurka, na kallon kan ta a matsayin mafi kwarewa, wadda kuma ta cancanci ta koyar da duniya yadda ake kare hakkokin dan adam, har ma a wasu lokutan yan siyasar ta ke nuna yatsa ga sauran sassa, kan yadda suke aiwatar da na su manufofin na kare hakkin bil adama.

To amma Bahaushe kan ce Mai daki shi ya san inda yake masa yoyo, wato dai ko wace kasa, ita ta fi sanin yanayi mafi dacewa na matakan da za ta iya aiwatarwa domin kare alummar ta daga fadawa rikici, ko gurguncewar hakkin alummar ta.

Kaza lika, a yayin da Amurka ke sukar sauran sassa da gazawa wajen kare hakkokin alumma, kamata ya yi ta fara duba matsalolin ta na cikin gida, kamar batun nuna wariyar launin fata da ya zama ruwan dare a kasar.

Masharhanta na cewa, alamar ci gaban alumma na bayyana ne daga imanin alumma da makomar su.

Wani sharhi da jaridar Washington Post ta wallafa a baya bayan, ya nuna sakamakon wani bincike da aka gudanar game da wariyar launin fata a Amurka, wanda ya tabbatar da cewa, kaso mafi rinjaye na Amurkawa masu asali daga Afirka sun damu, da yadda ake samun karuwar nuna wariyar launin fata gare su a shekarun baya bayan nan, sama da yadda abun yake a baya.

Kaza lika, sakamakon binciken ya nuna rashin gamsuwa da wannan rukuni na alummar Amurka ke da shi don gane da kyautatuwar yanayin kare hakkokin su, ciki har da na zamantakewa, da rashin daidaito a fannin tattalin arziki, da kula da lafiya, da batun fuskantar hare haren bindiga da dai sauran su.

Idan mun yi laakari da sakamakon wannan bincike, za mu iya gano cewa, Amurka na da na ta manyan matsaloli na kare hakkin dan adam, wadanda ya kamata ta tunkara, maimakon mayar da hankali ga sukar yadda wasu kasashen na daban ke kokari karewa alummun su hakkoki. Idan kuwa Amurka ba ta dauki wannan mataki ba, to sakamakon da za ta ci gaba da samu a cikin gida, zai dada tabbatar da kallon da wasu masu fashin baki ke mata, na mai take laifin ta domin hangen na wasu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Sheikh Jassim Ya Kusa Zama Sabon Mamallakin Man Utd

Next Post

Shari’ar Zaɓe: Gwamnan Sokoto Ya Kori Sakatarorin Ilimi Na Jihar

Related

Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa
Daga Birnin Sin

Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa

10 hours ago
Kasar Sin Na Da Muradin Zurfafa Hadin Gwiwar BRI Da Masar 
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Na Da Muradin Zurfafa Hadin Gwiwar BRI Da Masar 

11 hours ago
Wang Yi Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka
Daga Birnin Sin

Wang Yi Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka

13 hours ago
Fahimtar Kyawun Bambance-Bambance Kyakkawar Hanya Ce Ta Wanzar Da Zaman Jituwa A Duniya
Daga Birnin Sin

Fahimtar Kyawun Bambance-Bambance Kyakkawar Hanya Ce Ta Wanzar Da Zaman Jituwa A Duniya

14 hours ago
FRCN Ya Kaddamar Da Shirin Koyar Da Sinanci Mai Taken “Hello China”
Daga Birnin Sin

FRCN Ya Kaddamar Da Shirin Koyar Da Sinanci Mai Taken “Hello China”

15 hours ago
An Fitar Da Sanarwar Beijing Bayan Taron Ministocin Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Wayewar Kan Bil Adama
Daga Birnin Sin

An Fitar Da Sanarwar Beijing Bayan Taron Ministocin Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Wayewar Kan Bil Adama

16 hours ago
Next Post
Shari’ar Zaɓe: Gwamnan Sokoto Ya Kori Sakatarorin Ilimi Na Jihar

Shari'ar Zaɓe: Gwamnan Sokoto Ya Kori Sakatarorin Ilimi Na Jihar

LABARAI MASU NASABA

Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma

Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma

July 12, 2025
Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa

Rashin Ganin Shugabannin APC Yayin Ziyarar Shettima A Kano Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

July 12, 2025
Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa

Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa

July 11, 2025
Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya

Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya

July 11, 2025
Kasar Sin Na Da Muradin Zurfafa Hadin Gwiwar BRI Da Masar 

Kasar Sin Na Da Muradin Zurfafa Hadin Gwiwar BRI Da Masar 

July 11, 2025
Nijeriya Na Fuskantar Siyasa Mara Tabbas —  Peter Obi

2027: Takarar Shugaban Kasa Zan Yi Ba Mataimaki Ba – Peter Obi

July 11, 2025
“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai

“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai

July 11, 2025
2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a

2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a

July 11, 2025
Wang Yi Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka

Wang Yi Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka

July 11, 2025
Fahimtar Kyawun Bambance-Bambance Kyakkawar Hanya Ce Ta Wanzar Da Zaman Jituwa A Duniya

Fahimtar Kyawun Bambance-Bambance Kyakkawar Hanya Ce Ta Wanzar Da Zaman Jituwa A Duniya

July 11, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.