Ma’aikatar kula da harkokin cinikayya ta kasar Sin, ta sanar da matakan mayar da martani kan jerin munanan matakan da hukumar kula da sadarwa ta kasa da ma’aikatar kula da tsaron cikin gida na Amurka, suka dauka kan kasar Sin.
A cewar ma’aikatar, matakan hukumar kula da sadarwa ta Amurka da sanya wasu kamfanoni Sin cikin jadawalin Amurka na “dokar dakile tilastawa ‘yan kabilar Uygur kwadago” da ma’aikatar tsaron cikin gida ta Amurkar ta dauka, sun keta muhimmiyar matsayar da shugabannin kasashen biyu suka cimma, haka kuma suna illa ga ‘yanci da muradun kasar Sin.
Ma’aikatar ta ce ba abun da kasar Sin za ta yi face mayar da martani, ciki har da karfafa takaita fitar wa Amurka kayayyakin da suka shafi jirage maras matuki da ake iya amfani da su a harkokin yau da kullum da kuma na soji, da kaddamar da bincike kan kayayyakin aikin ofis masu manhajar kasashen waje da ake shigo da su kasar Sin, tana mai sanar da mayar da martani kan kamfanoni 6 na Amurka.
Ma’aikatar ta kara da cewa, Sin na bukatar Amurka ta gaggauta janye matakan da ta dauka, ta kuma dakatar da ayyukanta marasa dacewa. Amma idan Amurka ta nace kan daukar sabbin matakan da ba su dace ba, to ita ma za ta ci gaba da mayar da martani. (Mai fassara: Fa’iza Mustapha)














