Mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin, Lin Jian, ya bayyana a gun taron manema labarai da aka yi a yau Litinin 27 ga watan nan cewa, kasarsa na adawa da duk wani yunkuri na sanya takunkumin bangare guda kacal ba bisa doka ba.
Jami’in ya yi wannan furucin ne don mayar da martani game da takunkumin da kasar Amurka ta sanya wa wasu kamfanonin kasar Sin bisa hujjar da ta shafi kasar Iran, inda ya bukaci Amurka ta dakatar da sanya takunkumi ta hanyar da ba ta dace ba, tare da yin amfani da dokokinta kan mutane ko kamfanoni na sauran kasashe.
Jami’in ya kuma jaddada cewa, Sin za ta tsaya tsayin daka kan kiyaye halastattun hakkokin kamfanoninta.Sai dai kuma game da batun harbin da aka yi a fadar White House, jami’in Lin Jin ya ce, Sin tana maida hankali a kan batun, tare da adawa gami da Allah wadai da ire-iren ayyukan tada hankali ba bisa doka ba. (Murtala Zhang)















Discussion about this post