ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kisan Woro A Jihar Kwara Ya Bayyana Rugujewar Tsaron Karkara A Nijeriya — Gbenga Hashim

by Bello Hamza and Sulaiman
7 months ago
Kwara

Dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar Peoples Democratic Party (PDP), Dr. Gbenga Hashim, ya bayyana hare-haren kisan gillar da aka yi a garin Woro na Jihar Kwara a matsayin babban gargadi kan yadda al’ummomin karkara ke cikin hadari a Najeriya. Ya yi gargadin cewa kasar na iya fadawa wani zamani da hare-haren jama’a ke faruwa ba tare da daukar mataki cikin gaggawa ko kuma amsa mai tasiri daga gwamnati ba.

A cikin wata sanarwa da ya fitar a karshen mako, Hashim ya ce girman harin ya wuce a tsaya kan ta’aziyya kawai, yana mai kira da a dauki matakin tabbatar da gaskiya da rikon amana daga hukumomin tsaro.

  • Shin Ko Lokacin Lashe Firimiyar Arsenal Ya Yi?
  • IS Ta Fitar Da Bidiyon Harin Da Ta Kai Kan Sansanonin Soji A Yamai

“Wannan kisan ba shi da misali ta fuskar girma kuma babu kamarsa wajen rashin tausayi. Ina mika ta’aziyyata ga al’ummar Woro, amma ta’aziyya kadai ba ta isa ba a wannan karon,” in ji shi.

ADVERTISEMENT

Hashim ya bukaci wakilin Majalisar Dinkin Duniya na musamman kan harkokin kare hakkin bil’adama da ya fara bincike na kasa da kasa kan lamarin, yana mai cewa jama’a na da hakkin sanin dalilin da ya sa aka yi zargin watsi da bayanan sirri game da harin.

A cewarsa, wannan bala’i ya nuna yadda mutanen karkara suka zama masu rauni.

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Yusuf Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Gano Waɗanda Suka Kashe Danshagamu

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

“Kisan Woro ya nuna yadda ya zama abu mai sauki ga wasu gungun mahaukata su hallaka daruruwan rayuka ba tare da turjiya ba,” in ji shi.

Tsohon dan takarar shugaban kasar ya kuma nuna damuwa kan rashin daukar matakin tallafin jiragen sama yayin harin, yana mai cewa karfin sojojin saman Najeriya ya kamata ya sa hujjar ‘nisantar wuri’ ba ta zama karbabbiya ba.

Da yake magana kan kasancewar rundunar sojin sama ta Najeriya a yankin Wawa–New Bussa, wanda ya ce bai wuce mintuna 15 na tashi ba daga Woro, Hashim ya tambayi dalilin da ya sa ba a tura agajin gaggawa ta sama ba.

“Na ji bayanin da ba za a amince da shi ba cewa ana daukar sa’o’i kafin a isa kauyen mai nisa. To me ya faru da Sojojin Sama?” ya tambaya.

Hashim ya kuma yi nuni da abin da ya kira sabani a yadda sojoji ke mayar da martani, yana tunatar da ayyukan da suka taba yi a kasashen waje.

“Duniya na bukatar sanin dalilin da ya sa Sojojin Saman da suka iya tashi zuwa Jamhuriyar Benin domin ceton shugabanta daga bore ba su iya ceton mutanen Woro a yankin nan ba,” in ji shi.

Ya kuma soki manyan hafsoshin soja, yana mai cewa rundunar sojin Najeriya ta taba taka rawar gani a rikice-rikicen yankin kamar na Saliyo da Laberiya.

“Halin da manyan hafsoshin soja suka nuna bai kai matsayin da ake sa ran Najeriya ba. Sojojinmu sun dakatar da kashe-kashe a Saliyo da Laberiya a baya. Me ya sa ba za su iya dakatar da kashe ’yan Najeriya a cikin al’ummominsu ba?” ya tambaya.

Hashim ya ce rahotanni sun nuna cewa maharan sun aika da wasikar barazana ga al’ummar, kuma an sanar da hukumomi. Ya kuma tambayi batun cewa an tura sojoji amma daga bisani aka janye su.

’“Yan Najeriya na da hakkin sanin wanda ya bayar da umarnin janyewar da kuma dalilin yin hakan,” in ji shi.

Ya bayyana rahotannin da ke cewa an sanar da hukumomin tsaro yayin da harin ke gudana amma suka iso ne bayan maharan sun tsere a matsayin abin matukar tayar da hankali, yana tambayar yadda kusan mutane 200 za su iya rasa rayukansu ba tare da kama ko samun sahihan bayanai kan masu laifin ba har bayan kwanaki.

Hashim ya yi gargadin cewa jinkirin mayar da martani daga hukumomin tsaro na kara karfafa gwiwar maharan tare da fadada gibin amana tsakanin jama’a da gwamnati.

“Wannan ita ce masifar karkarar Najeriya a yau. Ana kai wa ’yan kasa hari, amma gwamnati na zuwa ne bayan an gama, ba lokacin da ake yi ba,” in ji shi.

Ya kuma yi gargadin cewa gazawar kare al’ummomin da ke nesa na iya tilasta mazauna su dauki matakan kare kai da kansu, ciki har da daukar fansa ta ’yan banga, nuna wariyar kabila, da kafa kungiyoyin makamai ba tare da tsari ba.

“Idan al’umma suka ji an watsar da su, za su fara neman tsira a wajen gwamnati. Hakan ne ke jefa al’umma cikin karin rashin kwanciyar hankali,” ya yi gargadi.

Hashim ya bukaci Gwamnatin Tarayya, Rundunar Sojin Sama ta Najeriya, da sauran hukumomin tsaro su gabatar da cikakken bayani kan yadda aka gudanar da ayyukan a lokacin harin, ciki har da jadawalin kiran gaggawa, matakan da aka dauka, da dalilan rashin tura jiragen sama.

Ya kuma ba da shawarar a yi garambawul domin karfafa tsaron karkara ta hanyar samar da tsarin mayar da martani cikin gaggawa, sa ido ta sama, tura jirage masu saukar ungulu, da kafa sansanonin aiki a yankunan iyaka masu hadari.

A cewarsa, bai kamata a dauki kisan Woro a matsayin wani lamari kadai ba, illa a gan shi a matsayin alamar karuwar rashin tsaro a yankin Arewa ta Tsakiya, musamman a al’ummomin da ke makwabtaka da Jihar Neja da yankin Tafkin Kainji.

Ya yi gargadin cewa idan ba a dauki mataki mai karfi ba, Jihar Kwara na iya zama sabon sahun gaba na ayyukan ’yan bindiga da ta’addancin karkara, lamarin da zai yi barazana ga noma, hanyoyin samun abinci, da zaman lafiyar al’umma.

“Bai kamata Najeriya ta saba da kashe-kashen jama’a ba. Idan ana iya kai hari ga wani kauye na tsawon sa’o’i ba tare da gwamnati ta mayar da martani ba, to muna fuskantar babbar matsalar gaggawa ta kasa,” in ji Hashim.

Kwara
Bello Hamza
+ posts Bio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Jihar Kano Za Ta Amfana Matuka Da Gidauniyar Aliko Dangote – Masu Ruwa Da Tsaki
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    An Nuna Damuwa Kan Sake Kamun Da DSS Ta Yi Wa Boɗejo Bayan Samun Belin EFCC
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Dole Al’ummar Arewa Su Rungumi Hanyoyin Kasuwanci Na Zamani —Alfa Musa
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Ba Mu Taba Biyan Kudin Fansa Ba Kuma Ba Za Mu Biya Ba – Kwamishinan Katsina
Kwara
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna
  • Sulaiman
    Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba
  • Sulaiman
    Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa
  • Sulaiman
    Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

MASU ALAKA

Labarai

Gwamna Yusuf Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Gano Waɗanda Suka Kashe Danshagamu

September 10, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu
Labarai

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

September 9, 2026
Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu
Manyan Labarai

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

September 9, 2026
Next Post
Ma’aikatar Wajen Sin Ta Maida Martani Kan Mummunan Harin Bam Da Aka Kai Pakistan

Ma’aikatar Wajen Sin Ta Maida Martani Kan Mummunan Harin Bam Da Aka Kai Pakistan

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Yusuf Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Gano Waɗanda Suka Kashe Danshagamu

September 10, 2026
Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

September 9, 2026
Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

September 9, 2026
Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

September 9, 2026
Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

September 9, 2026
Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

September 9, 2026
Bikin CIFTIS Zai Ingiza Bude Kofa A Kasar Sin

Bikin CIFTIS Zai Ingiza Bude Kofa A Kasar Sin

September 9, 2026
“Ajin Tashar Sararin Samaniya Na Hong Kong Da Macau” Ya Kara Wa Matasa Sha’awar Kimiyya Da Karfafa Kishin Kasa

“Ajin Tashar Sararin Samaniya Na Hong Kong Da Macau” Ya Kara Wa Matasa Sha’awar Kimiyya Da Karfafa Kishin Kasa

September 9, 2026
’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja

’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja

September 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.