• English
  • Business News
Tuesday, July 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ko Kin San… Sirrikan Nuna Soyayya Ga Miji?

by Sulaiman, CGTN Hausa and Bilkisu Tijjani
11 months ago
in Uwargida Sarautar Mata
0
Ko Kin San… Sirrikan Nuna Soyayya Ga Miji?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Assalamu alaikum masu karatu, barkan mu da sake haduwa daku a wannan makon a cikin shirin na mu mai farin jini da albarka na Ko Kin San.

A yau shafin na mu zai yi magana ne akan yadda wasu mata suka dauki kansu da cewa wai su sun girmi yin soyayya.

 

Wai sun girma ba a soyayya:

Yanzu dai bari na fara da ke uwargida; Ya kamata ki saurari duk nasihohin da zan miki, ki gode wa Allah wurin yin amfani da baiwar da ya yi miki, na kasancewa uwargida, wato komai dai yana hannunki ne har da shi kansa maigidan naki, a daidai wannan gabar in ka ji mace tana kukan yadda sitiyarin maigidan ya yi karfi, har ta kai ga cewa ba ta iya juyawa, to ta binciki kanta.

Labarai Masu Nasaba

Kula Da Kanki Bayan Haihuwa Abu Ne Muhimmi

Kar Ki Bari Naman Sallah Ya Kashe Miki Aure Yar’uwa

 

Hakika Allah S.W.T yana cewa:

“An kawata wa mutane son ababan sha’awa daga mata”.

Asali ke abar sha’awa ce ko kin yi ado ko ba ki yi ba, to me zai sa ba za ki yi adon domin ki karkato da hankalin maigidanki zuwa gare ki ba. Wasu matan su kan kalli wasan kwaikwayon Indiya sai su rika sha’awar yadda maza suke ma’amalla da matansu, wasu kuma wasu kuma wasan kwaikwayon Hausa suke kallo, to amma akwai wani abin lura, shi ne, shin mu a wannan matattarar tamu, mace ta kan kure adaka ta sha turare ga lalle yana daukar hankali, ta saka kayan da za su rika fizgar hankalin mai kallo don kawai ta yi rawa a gaban maigidanta ta tayar masa da sha’awarsa ya ji yana bukatarta.

Mai yuwuwa wani ya ce wannan al’adar Yahudu da Nasara ce, ko ita matar malam Bahaushe ta ce haba wannan ai sai yara mu mun girma ko ta ce sai kuma a ganki tsofai-tsofai da ke ga yara sun isa aure kina yi wa maigida rawa to amma kuma tana bukatar soyayyarsa.

Asshaikh Nasiruddeen Al’Albani RH ya fitar da wata fatawa a cikin majallar (Mujallatul Asaalah 8/ 74) yake cewa rawar da mace za ta yi a gaban maigidanta rawa kawai da aka saba ba wai na gaban jama’a ba (ba wai a wasan kwaikwayo da wuraren bukukuwa ba), kuma ba koyo ta yi masamman don ta rika yi ana gani ba, wannan ko da za ta motsa sha’awar maigida babu wani nassi da ya haramta, amma da sharadin cewa daga ita sai maigidanta kawai.

An tambayi malam cewa: To in ta saka irin kayan da masu rawa a wasannin kwaikwayo suke sakawa tsaya a gaban mijinta, ashe wannan ba koyi da su take yi ba, kuma da nuna kauna ga abin da suke yi, sai ya ce “Wannan halas ne matukar a tsakankanin ma’auratan ne, kuma ba wani ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Saka Ya Saka Murmushi A Fuskar Magoya Bayan Arsenal

Next Post

Ambaliya: Gwamna Dauda Lawal Ya Nuna Alhini Da Mika Jaje Ga Al’ummar Gummi

Related

Wasu Abubuwa Da Ke Sa Maza Hana Mata Fita Unguwa (Uwargida)
Uwargida Sarautar Mata

Kula Da Kanki Bayan Haihuwa Abu Ne Muhimmi

3 weeks ago
aure
Uwargida Sarautar Mata

Kar Ki Bari Naman Sallah Ya Kashe Miki Aure Yar’uwa

1 month ago
Soyayya
Uwargida Sarautar Mata

Hanyoyi Goma Sha Daya Da Mace Za Ta Bi Domin Janyo Hankalin Mijinta

4 months ago
Soyayya
Uwargida Sarautar Mata

A Rungumi Hakuri A Zaman Aure ‘Yan’uwa Mata

5 months ago
aure
Uwargida Sarautar Mata

Mu Tsare Martabar Aure Don Kiyaye Makomarmu

8 months ago
Wasu Abubuwa Da Ke Sa Maza Hana Mata Fita Unguwa (Uwargida)
Uwargida Sarautar Mata

Yadda Za Ki Burge Miji Kuma Ki Sa Masa Kaunarki

8 months ago
Next Post
Ambaliya: Gwamna Dauda Lawal Ya Nuna Alhini Da Mika Jaje Ga Al’ummar Gummi

Ambaliya: Gwamna Dauda Lawal Ya Nuna Alhini Da Mika Jaje Ga Al'ummar Gummi

LABARAI MASU NASABA

Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa

Nijeriya Ba Ta Da Sha’awar Yin Gwajin Makamin Nukiliya — Shettima

July 8, 2025
Da Ɗumi-Ɗumi: Osimhen Ya Amince Da Komawa Galatasaray Na Dindindin

Da Ɗumi-Ɗumi: Osimhen Ya Amince Da Komawa Galatasaray Na Dindindin

July 7, 2025
Sin Za Ta Ci Gaba Da Karfafa Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Kan Tinkarar Sauyin Yanayi

Sin Za Ta Ci Gaba Da Karfafa Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Kan Tinkarar Sauyin Yanayi

July 7, 2025
Ƙungiyar Al’ummar Igbo Ta Ohanaeze Ndigbo Ta Ce Tinubu Ya Fi Ƙarfin ‘Yan Jam’iyyar Haɗaka Ta ADC

Ƙungiyar Al’ummar Igbo Ta Ohanaeze Ndigbo Ta Ce Tinubu Ya Fi Ƙarfin ‘Yan Jam’iyyar Haɗaka Ta ADC

July 7, 2025
Sin Za Ta Gina Wuraren Cajin Ababen Hawa Masu Ingantaccen Lantarki

Sin Za Ta Gina Wuraren Cajin Ababen Hawa Masu Ingantaccen Lantarki

July 7, 2025
NiMet Ta Yi Hasashen Cikin Watan Yulin 2025 Za A Tabka Ambaliyar Ruwan Sama A Jihohin Nijeriya 19

NiMet Ta Yi Hasashen Cikin Watan Yulin 2025 Za A Tabka Ambaliyar Ruwan Sama A Jihohin Nijeriya 19

July 7, 2025
Sin Ta Kafa Kungiyar Masana Masu Binciken Sararin Samaniya Mai Zurfi Ta Farko

Sin Ta Kafa Kungiyar Masana Masu Binciken Sararin Samaniya Mai Zurfi Ta Farko

July 7, 2025
Xi Ya Ajiye Furanni Ga Wadanda Suka Mutu Yayin Yakin Bijirewa Harin Japan

Xi Ya Ajiye Furanni Ga Wadanda Suka Mutu Yayin Yakin Bijirewa Harin Japan

July 7, 2025
Asibiti Mai Zaman Kansa A Kano Zai Fara Aikin Manyan Tiyatu Tare Da Rage Kuɗi Kaso 50%

Asibiti Mai Zaman Kansa A Kano Zai Fara Aikin Manyan Tiyatu Tare Da Rage Kuɗi Kaso 50%

July 7, 2025
Shafin Yanar Gizo Na ADC Ya Tsaya Cak Saboda Ɗumbin Magoya Baya Masu Son Yin Rijista

Shafin Yanar Gizo Na ADC Ya Tsaya Cak Saboda Ɗumbin Magoya Baya Masu Son Yin Rijista

July 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.