ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ko Kin San…Yadda Za Ki Zauna Da Mijinki Mai Mata Fiye Da Daya?

by Bilkisu Tijjani and Sulaiman
2 months ago
Mata

Aure na da babbar hikima da daraja a musulunci, kuma Allah ya halatta wa maza su auri mata har hudu, idan har za su yi adalci. Idan mijinki yana da mata fiye da daya, ga wasu shawarwari da za su taimake ki don zaman lafiya da kwanciyar hankali.

1. Fahimtar Matsayinki a Aure:

Kamar yadda kowa yake da hakki a aure, ki san cewa Allah ne ya kaddara hakan.

ADVERTISEMENT

Idan mijinki ya kara aure, hakan ba yana nufin baya kaunarki ba.

Ki fahimci cewa Allah ne ya ce suyi, namiji daban yake da mace, don haka yana da bukatar kulawar mata fiye da daya.

LABARAI MASU NASABA

Nasiha Ga Uwargida Kan Zafin Kishi (2)

Nasiha Ga Uwargida Kan Zafin Kishi (1)

2. Kar ki ji kishi mai hana hakuri:

Kishi dabi’a ce ga mata, amma kada ya kai ga yin mugun hali.

Idan kika dinga kishi sosai, hakan zai hana ki nutsuwa kuma zai iya haifar da matsaloli da mijinki.

A yi kishi cikin hikima, ba tare da cin zalin wata daga cikin matan ba.

3. Yin hakuri da adalcin miji:

Miji yana da hakkin bai wa kowacce mace kulawa da lokaci, kudi da bukatun aure.

Idan ba zai iya zama da kowacce daidai ba, yana iya haifar da matsala.

Idan kina ganin yana nuna wariya, ki yi magana da hikima ba tare da hayaniya ba.

4. Kar ki yi kokarin rabawa da zuciya:

Wata mace idan mijinta ya kara aure, sai ta fara son ganin rabuwar sa da sabuwar matar.

Wannan ba daidai ba ne, domin Allah yana kin cutar da wani ba tare da hakki ba.

Idan mijinki yana adalci, ki runguma da zuciya daya.

5. Girmama ‘yar uwarki (Matar Mijinki):

Kamar yadda kike son ayi miki adalci, ita ma tana da hakkinta.

Ki guji yi mata zagon kasa ko tona mata asiri.

Ku zama ‘yan uwa, domin ku ne abin alfaharin juna.

6. Ki zauna lafiya da mijinki:

Ki yawaita kwalliya da gyaran jiki don ya ci gaba da jin dadin kasancewa da ke.

Ki guji magana mara dadi ko yawan gunaguni, don kada ki fusata shi.

Ki bi shi da ladabi da hikima, domin hakan yana sa miji ya kara son mace.

7. Dogara ga Allah da yin addu’a:

Idan kina jin damuwa ko matsala, ki dogara ga Allah.

Ki nemi shawara daga malamai idan matsalolin sun yi yawa.

Ki yawaita yin istighfari domin Allah ya daidaita muku zaman aure.

Zaman aure da kishiya ba abu ne mai sauki ba, amma idan kika dage da hakuri da hikima, za ki zauna lafiya. Allah ya albarkaci zaman ku, ya baku zuri’a mai albarka.

Shawara ga mace ta biyu ko mai niyya da shirin zama mata ta biyu:

Ki yi hakuri. Tabbas, bayan an kai ki, za ki fuskanci kalubale da dama. Zai yiwu ki ji kamar mijinki ya rage miki kulawa, ba kya samun isasshen lokaci da hankalinsa, kuma watakila ya fi bada lokaci ga matarsa ta farko. Wata rana kina tare da shi, amma yana ta waya da ita. Wani kuwa har bai iya daga wayarki idan yana wajenta. Irin wannan abubuwan na iya faruwa, kuma wani lokaci ma fiye da haka.

Ki yi hakuri. Ina tabbatar miki cewa yana cikin matsanancin hali. Yana kokarin shawo kan matarsa ta farko, domin a mafi yawan lokuta, maza ba su fahimci kissa da dabarun mata ba. Wasu matan suna amfani da kuka, marairaicewa, da neman tausayi wajen janyo hankalinsa. Wata kuwa tana nuna wa mijinta cewa an tauye mata hakkinta da auren da ya kara, wanda hakan ke sa shi jin cewa bai kyautata mata ba.

Abin da ya sa kika shigo da’irarta ya sa zai fi tausaya mata fiye da ke, musamman idan suna zaman lafiya. Idan kuwa suna da matsaloli tun kafin ya aureki, to shi ma yana iya fuskantar irin wannan hali daga gare ta.

Yadda za ki yi da lamarin:

Ki yi hakuri, ki ba su lokaci.

Kar ki yi korafi, kar ki nuna tashin hankali.

Kar ki ambaci sunanta ko matsalarta a cikin maganarki.

Ki kauda kai daga duk abin da suke yi.

Ina tabbatar miki, idan kika ci gaba da yin hakuri da kawaici, wata rana zai fara tunanin cewa bai kyauta miki ba. Zai soma tsarguwa da abubuwan da matar farko ke yi, har ya soma juyowa gare ki. A hankali, zai fara fahimtar sharrinta ko salon da take amfani da shi.

Idan kuwa kika dage da korafi da mita, zaifi ma jin tausayinta fiye da ke. Ki fahimta cewa hakuri ne kadai zai baki nasarar samun hakkinki, amma fada da tirjiya ba lallai su amfanar da ke ba.

In kuwa ba za ki iya hakuri da wannan ba, to ki shirya yin fada da ba lallai ki yi nasara akansa ba. Idan kuma baki shirya duk wani kalubale ba, to ki hawura da auren namiji mai mata.

Mata
Bilkisu Tijjani
+ posts Bio
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Nasiha Ga Uwargida Kan Zafin Kishi (2)
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Muhimmancin Shan Ruwa Ga Kyawun Fata
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Nasiha Ga Uwargida Kan Zafin Kishi (1)
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Yadda Ake Wainar Masara Da Miyar Yaji
Mata
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo
  • Sulaiman
    Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta
  • Sulaiman
    Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya
  • Sulaiman
    Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

MASU ALAKA

Nasiha Ga Uwargida Kan Zafin Kishi (2)
Uwargida Sarautar Mata

Nasiha Ga Uwargida Kan Zafin Kishi (2)

July 5, 2026
Mata
Uwargida Sarautar Mata

Nasiha Ga Uwargida Kan Zafin Kishi (1)

June 27, 2026
Wasu Abubuwa Da Ke Sa Maza Hana Mata Fita Unguwa (Uwargida)
Uwargida Sarautar Mata

Nasiha Ga Uwargida Kan Zafin Kishi (1)

June 21, 2026
Next Post
Abincin Da Ya Kamata Ku Ci Lokacin Al’ada

Abincin Da Ya Kamata Ku Ci Lokacin Al'ada

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.