ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ko Kin San…Yadda Za Ki Zauna Da Mijinki Mai Mata Fiye Da Daya?

by Bilkisu Tijjani and Sulaiman
4 weeks ago
Mata

Aure na da babbar hikima da daraja a musulunci, kuma Allah ya halatta wa maza su auri mata har hudu, idan har za su yi adalci. Idan mijinki yana da mata fiye da daya, ga wasu shawarwari da za su taimake ki don zaman lafiya da kwanciyar hankali.

1. Fahimtar Matsayinki a Aure:

Kamar yadda kowa yake da hakki a aure, ki san cewa Allah ne ya kaddara hakan.

ADVERTISEMENT

Idan mijinki ya kara aure, hakan ba yana nufin baya kaunarki ba.

Ki fahimci cewa Allah ne ya ce suyi, namiji daban yake da mace, don haka yana da bukatar kulawar mata fiye da daya.

LABARAI MASU NASABA

Abin Da Yake Kashe Matanmu Na Hausawa

Kafin Ki Nemi Saki, Nemi Amsar Waɗannan Tambayoyi Da Kanki

2. Kar ki ji kishi mai hana hakuri:

Kishi dabi’a ce ga mata, amma kada ya kai ga yin mugun hali.

Idan kika dinga kishi sosai, hakan zai hana ki nutsuwa kuma zai iya haifar da matsaloli da mijinki.

A yi kishi cikin hikima, ba tare da cin zalin wata daga cikin matan ba.

3. Yin hakuri da adalcin miji:

Miji yana da hakkin bai wa kowacce mace kulawa da lokaci, kudi da bukatun aure.

Idan ba zai iya zama da kowacce daidai ba, yana iya haifar da matsala.

Idan kina ganin yana nuna wariya, ki yi magana da hikima ba tare da hayaniya ba.

4. Kar ki yi kokarin rabawa da zuciya:

Wata mace idan mijinta ya kara aure, sai ta fara son ganin rabuwar sa da sabuwar matar.

Wannan ba daidai ba ne, domin Allah yana kin cutar da wani ba tare da hakki ba.

Idan mijinki yana adalci, ki runguma da zuciya daya.

5. Girmama ‘yar uwarki (Matar Mijinki):

Kamar yadda kike son ayi miki adalci, ita ma tana da hakkinta.

Ki guji yi mata zagon kasa ko tona mata asiri.

Ku zama ‘yan uwa, domin ku ne abin alfaharin juna.

6. Ki zauna lafiya da mijinki:

Ki yawaita kwalliya da gyaran jiki don ya ci gaba da jin dadin kasancewa da ke.

Ki guji magana mara dadi ko yawan gunaguni, don kada ki fusata shi.

Ki bi shi da ladabi da hikima, domin hakan yana sa miji ya kara son mace.

7. Dogara ga Allah da yin addu’a:

Idan kina jin damuwa ko matsala, ki dogara ga Allah.

Ki nemi shawara daga malamai idan matsalolin sun yi yawa.

Ki yawaita yin istighfari domin Allah ya daidaita muku zaman aure.

Zaman aure da kishiya ba abu ne mai sauki ba, amma idan kika dage da hakuri da hikima, za ki zauna lafiya. Allah ya albarkaci zaman ku, ya baku zuri’a mai albarka.

Shawara ga mace ta biyu ko mai niyya da shirin zama mata ta biyu:

Ki yi hakuri. Tabbas, bayan an kai ki, za ki fuskanci kalubale da dama. Zai yiwu ki ji kamar mijinki ya rage miki kulawa, ba kya samun isasshen lokaci da hankalinsa, kuma watakila ya fi bada lokaci ga matarsa ta farko. Wata rana kina tare da shi, amma yana ta waya da ita. Wani kuwa har bai iya daga wayarki idan yana wajenta. Irin wannan abubuwan na iya faruwa, kuma wani lokaci ma fiye da haka.

Ki yi hakuri. Ina tabbatar miki cewa yana cikin matsanancin hali. Yana kokarin shawo kan matarsa ta farko, domin a mafi yawan lokuta, maza ba su fahimci kissa da dabarun mata ba. Wasu matan suna amfani da kuka, marairaicewa, da neman tausayi wajen janyo hankalinsa. Wata kuwa tana nuna wa mijinta cewa an tauye mata hakkinta da auren da ya kara, wanda hakan ke sa shi jin cewa bai kyautata mata ba.

Abin da ya sa kika shigo da’irarta ya sa zai fi tausaya mata fiye da ke, musamman idan suna zaman lafiya. Idan kuwa suna da matsaloli tun kafin ya aureki, to shi ma yana iya fuskantar irin wannan hali daga gare ta.

Yadda za ki yi da lamarin:

Ki yi hakuri, ki ba su lokaci.

Kar ki yi korafi, kar ki nuna tashin hankali.

Kar ki ambaci sunanta ko matsalarta a cikin maganarki.

Ki kauda kai daga duk abin da suke yi.

Ina tabbatar miki, idan kika ci gaba da yin hakuri da kawaici, wata rana zai fara tunanin cewa bai kyauta miki ba. Zai soma tsarguwa da abubuwan da matar farko ke yi, har ya soma juyowa gare ki. A hankali, zai fara fahimtar sharrinta ko salon da take amfani da shi.

Idan kuwa kika dage da korafi da mita, zaifi ma jin tausayinta fiye da ke. Ki fahimta cewa hakuri ne kadai zai baki nasarar samun hakkinki, amma fada da tirjiya ba lallai su amfanar da ke ba.

In kuwa ba za ki iya hakuri da wannan ba, to ki shirya yin fada da ba lallai ki yi nasara akansa ba. Idan kuma baki shirya duk wani kalubale ba, to ki hawura da auren namiji mai mata.

Mata
Bilkisu Tijjani
+ posts Bio
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Nasihar Da Ya Dace Dukkan Iyaye Su Yi Wa ‘Yaƴansu Yayin  Aure?
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Abin Da Yake Kashe Matanmu Na Hausawa
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Kafin Ki Nemi Saki, Nemi Amsar Waɗannan Tambayoyi Da Kanki
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Ko Kin San… Cututtukan Da Man Ridi Ke Warkarwa?
Mata
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
  • Sulaiman
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
  • Sulaiman
    Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
  • Sulaiman
    Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

MASU ALAKA

Abin Da Yake Kashe Matanmu Na Hausawa
Uwargida Sarautar Mata

Abin Da Yake Kashe Matanmu Na Hausawa

May 30, 2026
Kafin Ki Nemi Saki, Nemi Amsar Waɗannan Tambayoyi Da Kanki
Uwargida Sarautar Mata

Kafin Ki Nemi Saki, Nemi Amsar Waɗannan Tambayoyi Da Kanki

May 24, 2026
aure
Uwargida Sarautar Mata

Kuskure Goma (10) Da Matan Aure Ke Yi A Gidan Miji

May 16, 2026
Next Post
Abincin Da Ya Kamata Ku Ci Lokacin Al’ada

Abincin Da Ya Kamata Ku Ci Lokacin Al'ada

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.