ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Komai Nisan Dare Gari Zai Waye

by CGTN Hausa and Sulaiman
6 months ago
Dare

Yadda sojojin kasar Amurka suka kutsa cikin kasar Venezuela, da sace shugaban kasar da matarsa a kwanan baya, ya nuna mana wani salon huldar kasa da kasa: Babbar kasa ta yi amfani da karfin tuwo wajen wulakanta, da shawo kan wata karamar kasa, da kwace dukiyoyinta yadda take so. A zahiri, wannan salon hulda ya yi hannun riga da bukatar tabbatar da daidaito da adalci a duniya, kuma ya saba da yanayin ci gaban al’ummar bil Adama.

Saboda halayyar mutum ta son ganin tabbatuwar adalci, al’ummun duniya suna Allah-wadai da kasar Amurka wadda ke daukar matakan zalunci, da yin kira da a kare hakkin Venezuela, da na sauran kananan kasashe. A sa’i daya kuma, batun ya sa ana kara fatan ganin wani misalin huldar kasa da kasa mai dacewa. Hakika ma iya cewa, huldar dake tsakanin kasar Sin da kasashen Afirka, wani misali ne mai kyau a wannan fanni.

Victor K’Onyango, shahararren dan jarida ne na kasar Kenya, wanda ya rubuta wani bayani da aka wallafa a jaridar “The Independent” ta kasar Uganda a kwanan baya, inda ya ce, cikin shekaru 20 da suka wuce, an gina dimbin hanyoyin mota, da layin dogo, da tashoshin jiragen ruwa, da yankunan masana’antu a kasashen Afirka. A cewarsa, wannan ci gaba ba aikin jin-kai da na tallafi ne suka haifar da su ba, dalilin cimma wadannan nasarori masu armashi, shi ne yadda kasashen Afirka suke yin hadin gwiwa da kasashen da suke kallonsu a matsayin abokai masu matsayin daidai-wa-daida. A ganin Victor K’Onyango, sauyin tunanin kasashen Afirka, daga dogaro kan samun tallafi daga ketare zuwa kulla huldar abota, ta riga ta zama tushen ci gaban masana’antun kasashen nahiyar. Kana huldar hadin gwiwa da aka kulla tsakanin Sin da Afirka tun tuni, ita ce babban dalilin da ya sa ake samun wannan sauyi na tunani.

ADVERTISEMENT

Kana a nasa bangare, Silence Charumira, babban editan shafin yanar gizo na “Africa News 24” na kasar Lesotho, shi ma ya rubuta wani bayani a kwanan baya, inda a cikinsa ya ce, huldar abota dake tsakanin kasashen Afirka da kasar Sin, ban da haifar da ci gaba a nahiyar Afirka, ta kuma yi amfani da wasu ka’idojinta na tushe, wato daidaito da cimma moriyar juna, da girmama ikon mulkin kan juna, da dai sauransu, wajen aza harsashi ga yunkurin kafa wani tsarin jagorancin duniya mafi adalci, da inganta kulawa da ayyuka daban daban.

A cewar Mista Charumira, alkaluma da misalan da aka samu cikin shekaru 5 da suka gabata, sun nuna yadda aka tabbatar da cikakken daidaito da adalci a huldar abota ta Sin da Afirka, inda ake ta gina kayayyakin more rayuwa, gami da samar da karin ma’aikata masu kwarewa; da kokarin dogoro da kai maimakon dogaro kan wasu; kana ana himmantuwa wajen raba fasahohi, maimakon tilasta wani bangare ya dauki wani salo na raya tattalin arziki da aka tilasta masa. A ganin Mista Charumira, huldar abota ta Sin da Afirka ta nuna cewa, za a iya maye gurbin salon raya tattalin arziki da na jagorancin duniya na baya, wanda ya ba kasashen yamma wani matsayi na jagora, kuma ya dace a dauki mataki don samar da sauye-sauye da ake son gani.

LABARAI MASU NASABA

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya

A daidai lokacin da nake rubuta wannan bayani, ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi, yana gudanar da ziyarar aiki a kasashen Habasha, da Somaliya, da Tanzania, gami da Lesotho, al’amarin da ya kasance karo 36 a jere, da ministan wajen kasar Sin ke ziyartar nahiyar Afirka a farkon duk sabuwar shekara. Ta wannan lamari za mu iya ganin sahihancin kasar Sin wajen karfafa zumunta tsakaninta da kasashen Afirka. Kana wannan sahihanci shi ma ya tabbatar da cewa, a ko da yaushe za a iya cin gajiyar huldar abota tsakanin Sin da Afirka.

Don tabbatar da makomar duniyarmu mai haske, ya kamata a yi kokarin samun karin huldodin kasa da kasa masu kama da huldar abota dake tsakanin Sin da Afirka. Idan dai a karkashin tasiri mai yakini da huldodin suka samar, kasashe masu tasowa za su iya karfafa hadin kansu a kai a kai, to, tabbas wata rana za a kai ga ganin bayan mulkin danniya da ake yi a duniya. Kamar dai yadda masu iya magana kan ce “Komai nisan dare gari zai waye.” (Bello Wang)

Dare
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje
Dare
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
  • Sulaiman
    Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi
  • Sulaiman
    Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba
  • Sulaiman
    Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

MASU ALAKA

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya
Ra'ayi Riga

Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya

June 19, 2026
A Yi Watsi Da Wannan “Mummunan Teburi”
Ra'ayi Riga

A Yi Watsi Da Wannan “Mummunan Teburi”

June 18, 2026
Next Post
APC Ga Atiku: Dimokuraɗiyyar Nijeriya Ba Ta Cikin Barazana

APC Ga Atiku: Dimokuraɗiyyar Nijeriya Ba Ta Cikin Barazana

LABARAI MASU NASABA

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.