ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Komai Nisan Dare Gari Zai Waye

by CGTN Hausa and Sulaiman
5 months ago
Dare

Yadda sojojin kasar Amurka suka kutsa cikin kasar Venezuela, da sace shugaban kasar da matarsa a kwanan baya, ya nuna mana wani salon huldar kasa da kasa: Babbar kasa ta yi amfani da karfin tuwo wajen wulakanta, da shawo kan wata karamar kasa, da kwace dukiyoyinta yadda take so. A zahiri, wannan salon hulda ya yi hannun riga da bukatar tabbatar da daidaito da adalci a duniya, kuma ya saba da yanayin ci gaban al’ummar bil Adama.

Saboda halayyar mutum ta son ganin tabbatuwar adalci, al’ummun duniya suna Allah-wadai da kasar Amurka wadda ke daukar matakan zalunci, da yin kira da a kare hakkin Venezuela, da na sauran kananan kasashe. A sa’i daya kuma, batun ya sa ana kara fatan ganin wani misalin huldar kasa da kasa mai dacewa. Hakika ma iya cewa, huldar dake tsakanin kasar Sin da kasashen Afirka, wani misali ne mai kyau a wannan fanni.

Victor K’Onyango, shahararren dan jarida ne na kasar Kenya, wanda ya rubuta wani bayani da aka wallafa a jaridar “The Independent” ta kasar Uganda a kwanan baya, inda ya ce, cikin shekaru 20 da suka wuce, an gina dimbin hanyoyin mota, da layin dogo, da tashoshin jiragen ruwa, da yankunan masana’antu a kasashen Afirka. A cewarsa, wannan ci gaba ba aikin jin-kai da na tallafi ne suka haifar da su ba, dalilin cimma wadannan nasarori masu armashi, shi ne yadda kasashen Afirka suke yin hadin gwiwa da kasashen da suke kallonsu a matsayin abokai masu matsayin daidai-wa-daida. A ganin Victor K’Onyango, sauyin tunanin kasashen Afirka, daga dogaro kan samun tallafi daga ketare zuwa kulla huldar abota, ta riga ta zama tushen ci gaban masana’antun kasashen nahiyar. Kana huldar hadin gwiwa da aka kulla tsakanin Sin da Afirka tun tuni, ita ce babban dalilin da ya sa ake samun wannan sauyi na tunani.

ADVERTISEMENT

Kana a nasa bangare, Silence Charumira, babban editan shafin yanar gizo na “Africa News 24” na kasar Lesotho, shi ma ya rubuta wani bayani a kwanan baya, inda a cikinsa ya ce, huldar abota dake tsakanin kasashen Afirka da kasar Sin, ban da haifar da ci gaba a nahiyar Afirka, ta kuma yi amfani da wasu ka’idojinta na tushe, wato daidaito da cimma moriyar juna, da girmama ikon mulkin kan juna, da dai sauransu, wajen aza harsashi ga yunkurin kafa wani tsarin jagorancin duniya mafi adalci, da inganta kulawa da ayyuka daban daban.

A cewar Mista Charumira, alkaluma da misalan da aka samu cikin shekaru 5 da suka gabata, sun nuna yadda aka tabbatar da cikakken daidaito da adalci a huldar abota ta Sin da Afirka, inda ake ta gina kayayyakin more rayuwa, gami da samar da karin ma’aikata masu kwarewa; da kokarin dogoro da kai maimakon dogaro kan wasu; kana ana himmantuwa wajen raba fasahohi, maimakon tilasta wani bangare ya dauki wani salo na raya tattalin arziki da aka tilasta masa. A ganin Mista Charumira, huldar abota ta Sin da Afirka ta nuna cewa, za a iya maye gurbin salon raya tattalin arziki da na jagorancin duniya na baya, wanda ya ba kasashen yamma wani matsayi na jagora, kuma ya dace a dauki mataki don samar da sauye-sauye da ake son gani.

LABARAI MASU NASABA

Abokin Jibi Shi Ne Aboki

Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka

A daidai lokacin da nake rubuta wannan bayani, ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi, yana gudanar da ziyarar aiki a kasashen Habasha, da Somaliya, da Tanzania, gami da Lesotho, al’amarin da ya kasance karo 36 a jere, da ministan wajen kasar Sin ke ziyartar nahiyar Afirka a farkon duk sabuwar shekara. Ta wannan lamari za mu iya ganin sahihancin kasar Sin wajen karfafa zumunta tsakaninta da kasashen Afirka. Kana wannan sahihanci shi ma ya tabbatar da cewa, a ko da yaushe za a iya cin gajiyar huldar abota tsakanin Sin da Afirka.

Don tabbatar da makomar duniyarmu mai haske, ya kamata a yi kokarin samun karin huldodin kasa da kasa masu kama da huldar abota dake tsakanin Sin da Afirka. Idan dai a karkashin tasiri mai yakini da huldodin suka samar, kasashe masu tasowa za su iya karfafa hadin kansu a kai a kai, to, tabbas wata rana za a kai ga ganin bayan mulkin danniya da ake yi a duniya. Kamar dai yadda masu iya magana kan ce “Komai nisan dare gari zai waye.” (Bello Wang)

Dare
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya
Dare
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
  • Sulaiman
    Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
  • Sulaiman
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
  • Sulaiman
    Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

MASU ALAKA

Abokin Jibi Shi Ne Aboki
Ra'ayi Riga

Abokin Jibi Shi Ne Aboki

June 3, 2026
Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka
Ra'ayi Riga

Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka

June 1, 2026
Nagartattun Manufofin Sin Suna Janyo Hankalin Kasashen Duniya
Ra'ayi Riga

Nagartattun Manufofin Sin Suna Janyo Hankalin Kasashen Duniya

May 29, 2026
Next Post
APC Ga Atiku: Dimokuraɗiyyar Nijeriya Ba Ta Cikin Barazana

APC Ga Atiku: Dimokuraɗiyyar Nijeriya Ba Ta Cikin Barazana

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.