Wata kotu a Abuja ta ba EFCC izinin kama tsohuwar ministar jin ƙai ta ƙasa, Sadiya Umar Farouq, bisa zargin badaƙalar kuɗi.
Hukumar EFCC na bincikenta ne kan zargin almundahanar da ta kai dala miliyan 1.3 da kuma naira miliyan 746.6 da ake zargin an wawure daga ma’aikatar jin ƙai.
El-Rufai Ya Ziyarci EFCC A Ranar Haihuwarsa
EFCC Ta Ɗauki Matakin Ƙwace Wasu Gidajen Abubakar Malami A Abuja
A cewar EFCC, mai shari’a Jude Onwuegbuzie ya kuma amince da kama sakataren ma’aikatar, Bashir Nura Alkali, bayan da suka gaza bayyana a gaban kotu.
Lauyoyin waɗanda ake zargi sun nemi a ba su uzuri saboda rashin lafiya da ya hana Sadiya halartar kotu, amma kotu ta yi watsi da buƙatar.
Rahotan BBC Hausa ya bayyana cewa EFCC ta shigar da ƙarar tun Disambar 2025, amma ta fuskanci ƙalubale wajen miƙa takardun ƙara ga waɗanda ake zargin domin fara shari’a.















Discussion about this post