Ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi, ya bayyana a jiya Laraba cewa, kasar Sin tana goyon bayan ci gaba da tattaunawar samun cikakkiyar tsagaita wuta da sulhu, wadda ta dace da muhimman muradun al’ummar kasar Iran, ta kuma yi daidai da kyakkyawan fatan kasashen yankin da ma sauran al’ummomin duniya.
Wang, mamba a ofishin siyasa na kwamitin tsakiya na jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin, ya bayyana hakan ne a lokacin da yake zantawa da ministan harkokin wajen Iran Seyed Abbas Araghchi ta wayar tarho.
Araghchi ya yi wa Wang karin bayani kan sabbin ci gaban da aka samu a tattaunawar Iran da Amurka da kuma abubuwan da Iran za ta yi la’akari da su.
Ya ce Iran ta yaba da kokarin da kasar Sin ke ci gaba da yi na rage zaman dar-dar a yankin, inda ya kara da cewa, Tehran na fatan Beijing za ta taka muhimmiyar rawa wajen samar da zaman lafiya da kawo karshen yakin baki daya.
A nasa bangaren, Wang ya ce, kasar Sin kamar ko da yaushe tana goyon bayan Iran wajen kare ’yancin kanta da tsaro da martabar yankunanta.
Ya kara da cewa, shugaba Xi Jinping ya gabatar da shawarwari guda hudu kan inganta zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin Gabas ta tsakiya, tare da ba da gudummawar dabara irin ta kasar Sin da za a yi amfani da ita wajen warware rikicin.
Ya kuma yi kira da a mutunta tare da kiyaye ’yancin kan kasar Iran da kuma halastattun hakkokinta a matsayinta na kasar da ke mashigin Hormuz, tare da tabbatar da ‘yanci da amincin zirga-zirgar jiragen ruwan kasa da kasa a mashigin. (Mai Fassara: Abdulrazaq Yahuza Jere)















Discussion about this post