Tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, ya amsa gayyatar Hukumar Yaki da Cin Hanci da Rashawa (EFCC), don bayyana yadda ya tafiyar da kudaden jihar a matsayin gwamna a ranar haihuwarsa, 16 ga Fabrairu.
Jigon Jam’iyyar ADC, ya isa EFCC ranar Litinin don amsa tambayoyi kan zargin cin hanci da rashawa da ke da alaƙa da gwamnatinsa.
- FIFA World Cup: Yau Nijeriya Za Ta San Makomarta
- Shugabannin Duniya Sun Taya Sin Murnar Sabuwar Shekarar Doki
Ya isa hedikwatar EFCC tare da ɗaruruwan magoya bayansa.
A cewar takardun shaidar ranar haihuwarsa, an haifi El-Rufai a ranar 16 ga Fabrairu 1960.
Da isowarsa Nijeriya a makon da ya gabata daga Masar, tsohon gwamnan Jihar Kaduna ya ce zai amsa gayyatar da EFCC ta yi masa ranar Litinin da ƙarfe 10:00 na safe.
Ya ce, hukumar EFCC ta gayyace shi a lokacin da yake wajen kasar amma lauyoyinsa sun rubuta wa hukumar cewa zai kasance a ofishinsu a ranar Litinin.















Discussion about this post