ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Manyan ‘Yan Siyasar Nijeriya Da Taurarunsu Za Su Haska A 2026

by Yusuf Shuaibu, Sulaiman and Sani Anwar
5 months ago
Siyasa

shekarar 2027 ne Nijeriya za ta gudanar da babban zabenta, wanda a 2026 ita ce shekarar da ake gudanar da yakin neman zabe da jawo hankalin masu jefa kuri’a da kuma sake zana taswirar siyasa. Bisa ga yadda abubuwa suke tafiya a yanzu, dukkan idanu za su kasance a kan wasu manyan ‘yan siyasa da tauraransu za ta haskaka a wannan sabuwar shekara.

 

Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu

ADVERTISEMENT

Bayan ya samu tikitin kai tsaye na jam’iyyarsa ta APC, don ya sake tsayawa takarar shugaban kasa karo na biyu, shekarar 2026 za ta kasance shekara mai matukar muhimmanci ga Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu. Lokacin mulkinsa na farko ya kasance an bayyana shi da gyare-gyaren tattalin arziki masu karfi irin su daga darajar naira da cire tallafin man fetur wanda ya janyo matsin tattalin arziki.

Mutane za su so ganin yadda zai sarrafa sakamakon wadannan manufofi masu tsauri ta hayar yaki nema zabe. Zuwa farkon shekarar 2026, matsin tattalin arziki da ake fuskanta za su zama makamin siyasa mafi karfi a kasar nan. A al’ada, ‘yan Nijeriya suna kada kuri’asu ne bisa lura da  asalin kabila da yanki, amma 2026 na iya nuna wani sauyi zuwa zaben da ake yin sa bisa gwazon gwamnati wajen samar da ababen more rayuwa.

LABARAI MASU NASABA

2027: Rashin Hadin Kan Atiku Da Obi Da Kwankwaso Na Iya Taimaka Wa Tazarcen Tinubu

Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya Sun Shiga Rudani A Yayin Da Wa’adin Mika Sunayen Mambobi Ya Shude

 

Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio

A yayin da majalisar dattawa ta 10 ke shiga mataki na karshe na kalandar majalisa ta 2025, Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio ya samu kansa a sarkakakiya na sake sauya kundin tsarin mulki. Kafin shekarar 2026, akwai wasu muhimman batutuwa da ke kan tebur. Mafi muhimmanci daga ciki su ne, kirkirar ‘yansandar jihohi don magance matsalar tsaro da ke karuwa a kasar.

Majalisar Dattawa na kokarin sanya gyara a kundin tsarin mulki domin bai wa jihohi izinin kafa nasu ‘yansanda. Wannan yana nufin bai wa gwamnonin jihohi da shugabannin kananan hukumomi ikon samar da tsaro a yankunansu. Wani abu da ya shafi wannan shi ne, bukatar kirkirar sabbin jihohi. A yanzu, wannan kokari ya kai kololuwa tare da gabatar da daruruwan shawarwari ga kwamitin sake kundin tsarin mulki na majalisa. Rahotanni sun nuna cewa majalisar dattawa ta samu bukatu fiye da 30 na kirkirar sabbin jihohi.

A kwanakin baya ne, Akpabio ya sake tayar da sabon fata kan kirkirar Jihar Ibadan, yana bayyana hakan a matsayin bukata ta jama’a yayin ziyararsa ga Olubadan na Ibadanland. A tarihi, kirkirar jiha abu ne mai wahala sosai, yana bukatar samun rinjaye kashi biyu bisa uku a cikin duka majalisar tarayya da majalisun jihohi guda 36. Masu ruwa da tsaki za su kasance cikin fatan ganin yadda wadannan al’amura za su wakana a shekarar 2026.

Hazalika, ana gudanar da manyan sauye-sauye a tsarin zabe don magance kura-kuren da aka gani a zabukan 2023. Don samun ingancin tsarin, akwai kudirin da aka gabatar kan yin zabukan shugaban kasa da gwamnoni a watan Nuwamba 2026 maimakon 2027. Muhimmin gyara da ake tattaunawa shi ne, warware dukkan shara’o’in a kotu kafin a rantsar da wanda ya ci zabe.

A matsayinsa na shugaban majalisar dattawa, ana kallon Akpabio a matsayin garkuwar dokoki ga fadar shugaban kasa. Tasirinsa a kudu maso kudu da ikon da yake da shi na tabbatar da cewa ajandar dokoki ta kasance mai amfani ga Tinubu ya sa ya shiga ciki wadanda taurarosu za ta haska a 2026.

 

Peter Obi

Yayin da Peter Obi ya bayyana komawarsa jam’iyyar ADC, a matsayin jam’iyyar hadin gwiwar jam’iyyun adawa, don cimma burin siyasarsa a 2027. Har yanzu yana daga cikin wadanda taurarosu za ta haska a ciki siyasar Nijeriya. Ba kamar Atiku Abubakar ba, wanda ya a hukumance ya yi murabus daga PDP kuma ya karbi katin ADC a wani taron da aka gudanar, Obi ya sauya sheka ne daga jam’iyyar LP.

Babban abin mamaki shi ne, ko Obi zai amice ya zama mataimakin takarar Atiku. Ya bayyana cewa zai yi takarar shugaba kasa ne kawai, duk da haka yana ci gaba da zama a tebur daya da Atiku a tarurrukan jam’iyyar ADC. Akwai jita-jita cewa Obi yana jiran sakamakon gyaran tsarin mulki, musamman sabon jadawalin dokar zabe ta 2025, kafin ya tsai da shawara.

A lokuta da dama Obi ya ambata cewa zai kasance zai yi wa’adi mulki guda ne na shekara hudu wajen farfado da kasar. Duk da haka, bai fayyace ko wannan tayin wani bangare ne na yarjejeniya don samun goyon bayan Atiku ko kuwa alkawari ne na musamman ga masu zabe ba. Shirin Obi zai tabata ne a lokacin babban taron ADC da ake sa ran za a yi a farkon shekarar 2026.

 

Rabiu Kwankwaso

Rabiu Kwankwaso yana ci gaba da tallata burinsa na siyasa, yana taka rawar gani a cikin siyasar Nijeriya wanda ke sa shi watakila ya yi rashin tabbas a siyasar 2027.

Yayin da Atiku da Obi suka sauya sheka zuwa ADC, Kwankwaso ya ci gaba da zama jam’iyyar NNPP a matsayin tsani mai karfi, ya ki shiga kowace hadakar jam’iyyun adawa.

A makon jiya, a ranar 20 ga Disamba, 2025, ya shirya babban taron NNPP a Abuja, inda ya yi alfahari cewa NNPP ita ce jam’iyyar mafi daidaito da tsara a Nijeriya, yana barrata ta da rikice-rikicen cikin gida na APC da PDP. Ya jaddada cewa burinsa na lashe zaben shugaban kasa a 2027, ba tare da zama dan takarar mataimakin shugaban kasa ga Atiku ko wani ba.

 

Rotimi Amaechi

Amaechi ya shafe ‘yan watannin karshe na 2025 yana kokarin dawo da kansa cikin siyasar Nijeriya ta hanyar haduwa da kungiyoyin kawance. A watan Yulin 2025, a hukumace ya sauya sheka zuwa jam’iyyar ADC kuma ya yi alkawarin fuskantar Shugaba Tinubu kai tsaye a 2027.

A halin yanzu, yana sanya kansa a matsayin daya daga ciki ‘yan takarar shugana kasa guda uku a jam’iyyar ADC. A kwanakin baya, an ga hotunan tallansa a biranen Arewa kamar Kaduna, inda ake bayyana shi a matsayin mutum daya da zai iya yi aikin. Duk da haka, masu nazarin siyasa suna ganin wannan yana kama da wani babban wasa, domin ba tare da samun goyon baya daga Jihar Ribas da zai kawo ba, karfinsa na tare da Atiku da Obi zai ragu sosai. Idan har sakamakon zaben kananan hukumomi na 30 ga Agusta, 2025 zai iya zama misali, tasirin Amaechi a matakin kasa yana cikin rauni tun daga 1999. Muhimmancinsa yanzu ya dogara kusan gaba daya ga nasarar hadin jam’iyyun adawa na kasa.

Rahotani su bayyana cewa yawancin tsoffin kwamishinansa da shugabannin kananan hukumominsa ko dai sun koma bagaren Wike ko kuma sun yi hadin kai da Gwamna Siminalayi Fubara. Ba tare da samun gagarumin goyan baya a gida ba, Amaechi ba zai yi tasiri ba. Sai dai kuma burinsa na zama shugaban kasa na tattare ne a shekarar 2026.

 

Nyesom Wike

Ministan Abuja, Nyesom Wike, ya kasance babban jarumin siyasa. Duk da yake yana aiki a cikin majalisar Tinubu, yana ci gaba da rike iko a wani babban bangare na PDP. A shekarar 2026, rawar da yake takawa mai nauyi wacce ta hada yin aiki ga shugaba kasa yayin da yake rike da kafar ‘yan adawa, za ta kasance daya daga cikin mafi rikitarwa a ayyukan da za a kalla.

 

Rauf Aregbesola

Rauf Aregbesola yana cikin manyan ‘yan siyasar kasar nan da tauraronsu za ta haska a wannan shekarar. Bayan an kore shi daga APC, ya kasance babban abokin Tinubu tare da wata shakka ba, ya karya dukkan alakarsa da gwamnatin Tinubu domin jagorantar siyasarsa. Rayuwarsa da muhimmancinsa a siyasar kasar nan suna dogara ne a kan Jiharsa ta Osun da sabon rawar da yake takawa a hadin gwiwar adawa.

A matsayinsa na sakataren jam’iyyar ADC na wucin gadi, yanzu yana kan gaba a cikin ‘yan adawa. Muhimmancin Aregbesola ya dogara gaba daya ne kan ko har yanzu zai iya kawo nasara a Osun. Yanzu haka yana yaki a bangare biyu. Na farko, hadin gwiwar dabaru da Aregbesola ya yi da Gwamna Ademola Adeleke a 2022 ya rushe. Adeleke wanda kwanan nan ya koma Jam’iyyar Accord ya bayyana cewa mulkin Aregbesola shi ne mafi muni a tarihin Osun.

Idan ADC ta kasa yin tasiri sosai a zaben gwamnan Osun na 2026, tasirin Aregbesola a siyasa zai ragu a matakin kasa. Zai shiga shekarar 2027 a matsayin shugaba mara tasiri a ciki gidasa.

 

Shugaban INEC, Farfesa Joash Amupitan

Ga shugaban hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC), Farfesa Joash Amupitan, zabukan 2026 na jihohin Ekiti da Osun za su kasance zakaran gwajin dafi a jagorancinsa. A matsayinsa na  kararren masani, Amupitan ya shiga wannan matsayin da umarni na sake gina amincewar jama’a bayan rikice-rikicen zabukan 2023. Zabukan 2026 na jihohin Osun da Ekiti su ne manyan gwaje-gwaje na farko kafin babban zaben 2027. Za a mai da hankali kan amfani da fasaha ba tare da matsala ba da kuma rashin son zuciyar hukumomin tsaro.

A tarihin, Jihar Osun tana daga cikin jihohi masu samun rikicin zabe, a zaben Jihar Osun zai gwada iyawar hukumar wajen sarrafa yanayi mai matukar kwantar da hankali da warware rikice-rikicen sakamako zabe a kan lokacin. Ya yi alkawarin gyara matsalolin da suka shafi na’urar zabe.

Masu kada kuri’a jihohin Osun da Ekiti za su kasance a shirye don ganin ko sakamakon za a dora shi nan take ta na’urar zabe. Idan Farfesa Amupitan bai samu damar gudanar da wata tsari mai inganci a wadannan jihohi biyu ba, ko shakku babu zai yi wahala ya samu nasara a zaben 2027. Akasin haka, gudanar da tsari a fili a Ekiti da Osun zai tabbatar da nadinsa a matsayin shugaba mai gyara kuma zai ba shi kima a siyasa da ake bukata don kula da zabukan kasa.

Siyasa
Yusuf Shuaibu
+ posts Bio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Masana Tattalin Arziki Sun Yi Watsi Da Rahoton NBS Kan Tattalin Arziki
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Alƙawarin Wa’adi Ɗaya Na Peter Obi Ya Raba Kawunan Ƴan Arewa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    ‘Yan Majalisar Wakilai 50 Da Suka Rasa Tikitin Takara A Zaɓen Fid Da Gwani Na APC
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Zaɓen Fitar Da Gwani: APC Na Fuskantar Barazanar Tawaye
Siyasa
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
  • Sulaiman
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
  • Sulaiman
    Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
  • Sulaiman
    Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
Siyasa
Sani Anwar
+ posts Bio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Sojoji Sun Ceto Mutum 92 Tare Da Daƙile Harin Ƴan Ta’adda A Borno
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Uzodimma: Babu Dimokraɗiyya Idan Babu Hamayya
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Alamomin Fara Ruɓewar Hannu Bayan Ɗorin Gida
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Ministocin Da Suka Ajiye Muƙamansu Ba Su Samu Tikitin Takara Ba

MASU ALAKA

Siyasa
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Rashin Hadin Kan Atiku Da Obi Da Kwankwaso Na Iya Taimaka Wa Tazarcen Tinubu

May 16, 2026
Adawa
Tambarin Dimokuradiyya

Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya Sun Shiga Rudani A Yayin Da Wa’adin Mika Sunayen Mambobi Ya Shude

May 15, 2026
Abincin Da Ya Kamata Ku Ci Lokacin Al’ada
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Hadakar ‘Yan Adawa Ta Rushe Yayin Da Tikitin Takarar Shugaban Kasa Ya Raba Kan Shugabannin ADC

May 9, 2026
Next Post
Tsarin Dokoki Ne Kan Gaba Wajen Samar Da Kyakkyawan Muhallin Kasuwanci

Tsarin Dokoki Ne Kan Gaba Wajen Samar Da Kyakkyawan Muhallin Kasuwanci

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.