ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sakon Da Aka Isar Bisa Yadda Zimbabwe Ta Fitar Da Sinadarin Lithium Sulfate Da Ta Sarrafa A Gida Zuwa Ketare

by CGTN Hausa and Sulaiman
2 months ago
Lithium

Kwanan nan, an samun labari mai muhimmanci daga Zimbabwe da ke canza tarihin bunkasar ma’adinai a Afirka. A karkashin taimakon kamfanonin Sin, a karon farko ne nahiyar Afirka ta samu nasarar fitar da sinadarin Lithium Sulfate da aka sarrafa a cikin gida. Wannan gagarumin ci gaba ne da Zimbabwe ta samu wajen fita daga kangin “hako ma’adinai kawai, ba tare da sarrafa su ba”, kuma sabon ci gaba ne da Sin ta samu a tarihi wajen taimaka wa kasashen Afirka dogaro da karfinsu don sarrafa ma’adinai da kuma fitar da su.

Allah ya albarci Afirka da albarkatun ma’adanai masu dimbin yawa a duniya, amma tun da dadewa, Afirka ta sha wahala wajen mayar da fa’idar albarkatun zuwa fa’idar ci gaba, har ma ta dade tana fuskantar matsalar “fitar da albarkatun kasa ba tare da riba mai dacewa ba”, sakamakon irin tsarin hako ma’adinai da Turawan yamma suka aiwatar a nahiyar.

Wannan gagarumin ci gaban hadin gwiwar Sin da Afirka ya ba da damar canza wannan yanayin, inda kamfanonin kasar Sin suka tsara jerin sana’o’i masu alaka a cikin gidan Zimbabwe, wanda ya baiwa Afirka damar samun kwaskwarima a bangaren sarrafa ma’adinin Lithium ya zama Lithium Sulfate, wanda ya kawo karshen tarihin Afirka na fitar da ma’adinan da aka hako ba tare da sarrafa su ba da kuma rashin ikon magana a harkar masana’antu.

ADVERTISEMENT

Don haka ma, Farfesa Carlos Lopes daga kwalejin nazarin mulki ta Nelson Mandela ta jami’ar Cape Town a kasar Afirka ta kudu ya ce, nasarar fitar da sinadarin Lithium Sulfate yana da matukar ma’ana, wanda ke nuna cewa Afirka ta yi ban kwana da tsohon tsarin hadin gwiwa iri yadda kasashen yamma ke kwace albarkatunta, kuma ba za ta kasance wurin samar da albarkatu kawai ba, kana ta sauya yanayinta na dogaro da jarin waje.Hakika darajar wannan ci gaba ta wuce batun kasuwanci, kuma alama ce da ke nuna hadin gwiwar Sin da Afirka ta shiga sabon mataki.

A baya, hadin gwiwar Sin da Afirka ya fi mayar da hankali kan “hadin gwiwar ababen more rayuwa” kamar hanyoyi da tashoshin wutar lantarki da tashoshin jiragen ruwa. Aikin sarrafa sinadarin Lithium da Sin da Zimbabwe suke yi cikin hadin gwiwa a wannan karo, alama ce da ke nuna yadda hadin gwiwar bangarorin biyu ya shiga sabon mataki na zurfafa hadewar masana’antu. Abin da bangaren Sin ya fitar ba jari ba ne kawai, cikakken tsari ne dake hada fasaha mai muhimmanci da ma’auni da tsarin samar da kayayyaki, kana da kasuwanni.

LABARAI MASU NASABA

“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka

Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?

Yanzu haka Zimbabwe na mallakar wani muhimmin bangare na samar da sabbin makamashi ta sinadarin Lithium, duba da cewa tana da tsarin da ke iya samar da sinadarin Lithium Sulfate har tan 50,000 a ko wace shekara, matakin da ya sa ta iya shawarwari da tsai da farashin sinadarin a kasuwannin duniya.

A halin yanzu, yawancin kasashe masu tasowa suna neman kubuta daga kangin da suke ciki na fitar da albarkatunsu da ba a sarrafa ba, da daga matsayinsu a tsarin masana’antu a duniya. Nasarar da Zimbabwe da Sin suka samu a wannan karo, ba wai kawai tarihi ne na ci gaban masana’antun ma’adinai ta Afirka ba, har ma ta kasance wani sako da kasashe masu tasowa ke aikewa cikin hadin kai na kawar da yanayin maras adalci da Turawan yamma ke jagoranta, da tabbatar da makomarsu tare da gina tsarin tattalin arziki na duniya mafi adalci.(Marubuciya: MINA)

Lithium
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030
Lithium
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
  • Sulaiman
    Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
  • Sulaiman
    An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”
  • Sulaiman
    Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

MASU ALAKA

“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka
Ra'ayi Riga

“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka

July 10, 2026
Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?
Ra'ayi Riga

Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?

July 9, 2026
Mu Leka Yadda Sin Ke Ba Da Misali Ga Duniya Wajen Raya Aikin Noma Da Kauyuka
Ra'ayi Riga

Mu Leka Yadda Sin Ke Ba Da Misali Ga Duniya Wajen Raya Aikin Noma Da Kauyuka

July 7, 2026
Next Post
INEC Ta Kara Wa’adin Karbar Katin Zabe

Kotu Ta Tabbatar INEC Na Da Ikon Fitar Da Jadawalin Zaɓe

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.