Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta tabbatar da tsohon Shugaban Majalisar Dattawa, David Mark, a matsayin Shugaban Jam’iyyar ADC na ƙasa.
Mai shari’a Musa Liman ya yi watsi da ƙarar da ɗan Majalisar Wakilai, Leke Abejide, ya shigar, yana mai cewa kotu ba ta da hurumin tsoma baki a harkokin cikin gida na jam’iyyar.
Kotun ta kuma ce Abejide bai nuna yadda aka take wata doka ko haƙƙi ba, sannan bai bi hanyoyin sasanta rikicin cikin jam’iyyar ba kafin ya garzaya kotu.
Kotun ta yanke cewa tsarin da ya bai wa David Mark shugabancin jam’iyyar da kuma tsohon Gwamnan Jihar Osun, Rauf Aregbesola, muƙamin Sakataren Jam’iyyar na ƙasa ya bi kundin tsarin mulkin ADC da kuma Dokar Zaɓe.
Haka kuma, ta ce miƙa shugabanci daga tsohon shugaban jam’iyyar, Ralph Nwosu, zuwa David Mark an yi shi bisa doka.
Kotun ta umarci Abejide ya biya kowanne daga cikin waɗanda aka shigar da ƙarar tarar Naira miliyan biyu, sannan ta ci lauyansa tarar Naira miliyan 10 bisa tanadin Dokar Zaɓe.
Abejide, ya nemi kotun ta soke naɗin David Mark da Aregbesola tare da hana INEC amincewa da su a matsayin shugabannin ADC.
Sai dai daga baya ya fice daga jam’iyyar ADC zuwa jam’iyyar APC mai mulki.














