ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, June 22, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Ta Gargaɗi Masu Ɓoye Gas Ɗin Girki

by Abubakar Sulaiman
1 hour ago

Gwamnatin tarayya ta yi kashedi mai ƙarfi ga masu harkar iskar gas na girki (LPG) da su gaggauta daina ɓoye gas ɗin ko kuma su fuskanci hukunci mai tsanani. Ƙaramin ministan albarkatun man Fetur (Gas), Ekperikpe Ekpo, ne ya bayyana hakan a lokacin wani taron gaggawa da masu ruwa da tsaki na harkar, inda ya ce gwamnati tana da ƙwararan hujjoji na nuna cewa ana boye gas ɗin domin janyo ƙarancinsa da kuma haifar da tsadar farashi.

Ministan ya bayyana cewa, koda yake akwai matsaloli na raguwar shigo da gas ɗin daga ƙasashen waje, da tashin dalar amurka, da tsadar sufuri, amma babban abin da ke ƙara ta’azzara lamarin shi ne yadda wasu ‘yan kasuwa ke son janyo ƙaranci min kayan da gangan. Ya jaddada cewa babban burin ma’aikatarsa shi ne tabbatar da cewa gas ɗin da ake samarwa a cikin gida ya wadata amfanin mazauna ƙasar gabanin fitar da shi waje, sannan ya ba da umarnin cewa bayanan da yake samu sun nuna gas ɗin watan Yuni zai wadaci kowa idan har aka rarraba shi cikin adalci.

A nasa ɓangaren, Shugaban Hukumar NMDPRA, Rabiu Umar, ya bayyana cewa hukumar ba za ta lamunci ganin ana fitar da gas ɗin zuwa waje ba ana barin ‘yan kasa cikin wahala ba alhalin kasar tana da dumbin arzikin gas. Ya ƙara da cewa hukumar ta riga ta fara sanya idanu kan farashin kuma za ta hukunta duk wani dillali ko mai jigilar kaya da aka kama yana ƙara farashi ba tare da ƙa’ida ba, tare da bayyana cewa sabbin matatun gas da ke tafe, kamar ta Seplat, za su kawo sauƙin farashi gabanin ƙarshen watan Yuli.

ADVERTISEMENT

Daga ƙarshe, Babbar Sakatariya, Patience Oyekunle, ta buƙaci ɗaukacin masu ruwa da tsaki da su haɗa kai wajen inganta harkar rarraba iskar gas ɗin tare da nuna gaskiya a farashi domin kare haƙƙin masu amfani da shi ba tare da gurgunta gwuiwar masu zuba jari ba.

Jami’an gwamnati sun tabbatar wa mahalarta taron cewa za su ci gaba da wallafa sunayen duk wani kamfani ko mutumin da aka kama da laifin ɓoye gas ɗin, kuma za a miƙa su ga hukumomin tsaro domin fuskantar hukunci.

LABARAI MASU NASABA

Kotu Ta Bayar Da Umarnin Tsare Sowore A Gidan Yarin Kuje

Yanzu-Yanzu: An Kashe Manoma 18 Da Raunata Wasu A Wani Sabon Hari A Filato

Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP
  • Abubakar Sulaiman
    Kotu Ta Bayar Da Umarnin Tsare Sowore A Gidan Yarin Kuje
  • Abubakar Sulaiman
    Yanzu-Yanzu: An Kashe Manoma 18 Da Raunata Wasu A Wani Sabon Hari A Filato
  • Abubakar Sulaiman
    Yanzu-Yanzu: Firaiministan Birtaniya Keir Starmer Ya Yi Murabus

MASU ALAKA

Kotu Ta Bayar Da Umarnin Tsare Sowore A Gidan Yarin Kuje
Labarai

Kotu Ta Bayar Da Umarnin Tsare Sowore A Gidan Yarin Kuje

June 22, 2026
Yanzu-Yanzu: An Kashe Manoma 18 Da Raunata Wasu A Wani Sabon Hari A Filato
Manyan Labarai

Yanzu-Yanzu: An Kashe Manoma 18 Da Raunata Wasu A Wani Sabon Hari A Filato

June 22, 2026
Yanzu-Yanzu: Firaiministan Birtaniya Keir Starmer Ya Yi Murabus
Labarai

Yanzu-Yanzu: Firaiministan Birtaniya Keir Starmer Ya Yi Murabus

June 22, 2026
Next Post
Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP

Jam'iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP

Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP

June 22, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Gargaɗi Masu Ɓoye Gas Ɗin Girki

Gwamnatin Tarayya Ta Gargaɗi Masu Ɓoye Gas Ɗin Girki

June 22, 2026
Kotu Ta Bayar Da Umarnin Tsare Sowore A Gidan Yarin Kuje

Kotu Ta Bayar Da Umarnin Tsare Sowore A Gidan Yarin Kuje

June 22, 2026
Yanzu-Yanzu: An Kashe Manoma 18 Da Raunata Wasu A Wani Sabon Hari A Filato

Yanzu-Yanzu: An Kashe Manoma 18 Da Raunata Wasu A Wani Sabon Hari A Filato

June 22, 2026
Yanzu-Yanzu: Firaiministan Birtaniya Keir Starmer Ya Yi Murabus

Yanzu-Yanzu: Firaiministan Birtaniya Keir Starmer Ya Yi Murabus

June 22, 2026
Sojoji Sun Ceto Mutanen Da Aka Sace, Sun Daƙile Hari A Kaduna Da Zamfara

Sojoji Sun Ceto Mutanen Da Aka Sace, Sun Daƙile Hari A Kaduna Da Zamfara

June 22, 2026
Fisatattun Matasa Sun Ƙone Wata Mata Ƙurmus Kan Jita-Jitar Satar Yara A Kaduna

Fisatattun Matasa Sun Ƙone Wata Mata Ƙurmus Kan Jita-Jitar Satar Yara A Kaduna

June 22, 2026

Mutane 842 Ne Suka Rasa Ransu, Aka Yi Garkuwa Da Sama Da 270 A Watan Mayu – Rahoto

June 21, 2026
PRP Ta Zargi Kwankwaso Da Saye Fom Ɗin Takarar  Jamiyyar

PRP Ta Zargi Kwankwaso Da Saye Fom Ɗin Takarar Jamiyyar

June 21, 2026
An Ƙaddamar Da Dakarun Tsaron Daji 2,187 A Bauchi

An Ƙaddamar Da Dakarun Tsaron Daji 2,187 A Bauchi

June 21, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.