ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, July 12, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Ta Gargaɗi Masu Ɓoye Gas Ɗin Girki

by Abubakar Sulaiman
3 weeks ago

Gwamnatin tarayya ta yi kashedi mai ƙarfi ga masu harkar iskar gas na girki (LPG) da su gaggauta daina ɓoye gas ɗin ko kuma su fuskanci hukunci mai tsanani. Ƙaramin ministan albarkatun man Fetur (Gas), Ekperikpe Ekpo, ne ya bayyana hakan a lokacin wani taron gaggawa da masu ruwa da tsaki na harkar, inda ya ce gwamnati tana da ƙwararan hujjoji na nuna cewa ana boye gas ɗin domin janyo ƙarancinsa da kuma haifar da tsadar farashi.

Ministan ya bayyana cewa, koda yake akwai matsaloli na raguwar shigo da gas ɗin daga ƙasashen waje, da tashin dalar amurka, da tsadar sufuri, amma babban abin da ke ƙara ta’azzara lamarin shi ne yadda wasu ‘yan kasuwa ke son janyo ƙaranci min kayan da gangan. Ya jaddada cewa babban burin ma’aikatarsa shi ne tabbatar da cewa gas ɗin da ake samarwa a cikin gida ya wadata amfanin mazauna ƙasar gabanin fitar da shi waje, sannan ya ba da umarnin cewa bayanan da yake samu sun nuna gas ɗin watan Yuni zai wadaci kowa idan har aka rarraba shi cikin adalci.

A nasa ɓangaren, Shugaban Hukumar NMDPRA, Rabiu Umar, ya bayyana cewa hukumar ba za ta lamunci ganin ana fitar da gas ɗin zuwa waje ba ana barin ‘yan kasa cikin wahala ba alhalin kasar tana da dumbin arzikin gas. Ya ƙara da cewa hukumar ta riga ta fara sanya idanu kan farashin kuma za ta hukunta duk wani dillali ko mai jigilar kaya da aka kama yana ƙara farashi ba tare da ƙa’ida ba, tare da bayyana cewa sabbin matatun gas da ke tafe, kamar ta Seplat, za su kawo sauƙin farashi gabanin ƙarshen watan Yuli.

ADVERTISEMENT

Daga ƙarshe, Babbar Sakatariya, Patience Oyekunle, ta buƙaci ɗaukacin masu ruwa da tsaki da su haɗa kai wajen inganta harkar rarraba iskar gas ɗin tare da nuna gaskiya a farashi domin kare haƙƙin masu amfani da shi ba tare da gurgunta gwuiwar masu zuba jari ba.

Jami’an gwamnati sun tabbatar wa mahalarta taron cewa za su ci gaba da wallafa sunayen duk wani kamfani ko mutumin da aka kama da laifin ɓoye gas ɗin, kuma za a miƙa su ga hukumomin tsaro domin fuskantar hukunci.

LABARAI MASU NASABA

Wasu Fusatattun Mutane Sun Lakaɗa Wa Mutum Biyu Duka Har Lahira A Kaduna

Ƴan Ƙwadago Sun Buƙaci Naira 300,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    NAF Ta Kai Hare-Haren Sama Kan Maboyar Ƴan Ta’adda A Borno
  • Abubakar Sulaiman
    Gwamnati Ta Shirya Gina Gidaje 20,000 Duk Shekara Haɗin Gwuiwar Jamus
  • Abubakar Sulaiman
    Mutum 1 Ya Mutu, 7 Sun Jikkata Yayin Da Ginin Majalisar Dokokin Gombe Ya Rufta
  • Abubakar Sulaiman
    Duk Da Faɗuwar Farashin Ɗanyen Mai Ƴan Nijeriya Na Fama Da Tsadar Man Fetur

MASU ALAKA

‘Lokaci Ya Yi Na Ɗaukar Mataki Kan Masu Yanke Hukunci Da Kansu’
Labarai

Wasu Fusatattun Mutane Sun Lakaɗa Wa Mutum Biyu Duka Har Lahira A Kaduna

July 12, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Labarai

Ƴan Ƙwadago Sun Buƙaci Naira 300,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

July 12, 2026
NiMet Ta Gargaɗi Jihohi 27 Kan Barazanar Ambaliyar Ruwa A Farkon Watan Yuli
Labarai

NiMet Ta Gargaɗi Jihohi 27 Kan Barazanar Ambaliyar Ruwa A Farkon Watan Yuli

July 12, 2026
Next Post
Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP

Jam'iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP

LABARAI MASU NASABA

‘Lokaci Ya Yi Na Ɗaukar Mataki Kan Masu Yanke Hukunci Da Kansu’

Wasu Fusatattun Mutane Sun Lakaɗa Wa Mutum Biyu Duka Har Lahira A Kaduna

July 12, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Ƴan Ƙwadago Sun Buƙaci Naira 300,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

July 12, 2026
NiMet Ta Gargaɗi Jihohi 27 Kan Barazanar Ambaliyar Ruwa A Farkon Watan Yuli

NiMet Ta Gargaɗi Jihohi 27 Kan Barazanar Ambaliyar Ruwa A Farkon Watan Yuli

July 12, 2026
2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Amince Da Jamilu Gwamna A Matsayin Gwamnan Gombe

2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Amince Da Jamilu Gwamna A Matsayin Gwamnan Gombe

July 12, 2026
NDLEA Ta Gargaɗi Masu Sana’ar Keke NAPEP Kan Ta’ammali Da Miyagun Ƙwayoyi

NDLEA Ta Gargaɗi Masu Sana’ar Keke NAPEP Kan Ta’ammali Da Miyagun Ƙwayoyi

July 12, 2026
inec

2027: INEC Ta Tsawaita Wa’adin Miƙa Sunayen ’Yan Takara

July 12, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Tallafa Wa Yara Masu Buƙatu Na Musamman Shi Ne Burina

July 12, 2026
Annalena Baerbock: Kasar Sin Babbar Mai Goyon Bayan Tsarin Mabambantan Bangarori Ce

Annalena Baerbock: Kasar Sin Babbar Mai Goyon Bayan Tsarin Mabambantan Bangarori Ce

July 11, 2026
Sin Ta Kalubalanci A Tabbatar Da Tsagaita Bude Wuta A Gabas Ta Tsakiya

Sin Ta Kalubalanci A Tabbatar Da Tsagaita Bude Wuta A Gabas Ta Tsakiya

July 11, 2026
Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027

July 11, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.