Gwamnatin tarayya ta yi kashedi mai ƙarfi ga masu harkar iskar gas na girki (LPG) da su gaggauta daina ɓoye gas ɗin ko kuma su fuskanci hukunci mai tsanani. Ƙaramin ministan albarkatun man Fetur (Gas), Ekperikpe Ekpo, ne ya bayyana hakan a lokacin wani taron gaggawa da masu ruwa da tsaki na harkar, inda ya ce gwamnati tana da ƙwararan hujjoji na nuna cewa ana boye gas ɗin domin janyo ƙarancinsa da kuma haifar da tsadar farashi.
Ministan ya bayyana cewa, koda yake akwai matsaloli na raguwar shigo da gas ɗin daga ƙasashen waje, da tashin dalar amurka, da tsadar sufuri, amma babban abin da ke ƙara ta’azzara lamarin shi ne yadda wasu ‘yan kasuwa ke son janyo ƙaranci min kayan da gangan. Ya jaddada cewa babban burin ma’aikatarsa shi ne tabbatar da cewa gas ɗin da ake samarwa a cikin gida ya wadata amfanin mazauna ƙasar gabanin fitar da shi waje, sannan ya ba da umarnin cewa bayanan da yake samu sun nuna gas ɗin watan Yuni zai wadaci kowa idan har aka rarraba shi cikin adalci.
A nasa ɓangaren, Shugaban Hukumar NMDPRA, Rabiu Umar, ya bayyana cewa hukumar ba za ta lamunci ganin ana fitar da gas ɗin zuwa waje ba ana barin ‘yan kasa cikin wahala ba alhalin kasar tana da dumbin arzikin gas. Ya ƙara da cewa hukumar ta riga ta fara sanya idanu kan farashin kuma za ta hukunta duk wani dillali ko mai jigilar kaya da aka kama yana ƙara farashi ba tare da ƙa’ida ba, tare da bayyana cewa sabbin matatun gas da ke tafe, kamar ta Seplat, za su kawo sauƙin farashi gabanin ƙarshen watan Yuli.
Daga ƙarshe, Babbar Sakatariya, Patience Oyekunle, ta buƙaci ɗaukacin masu ruwa da tsaki da su haɗa kai wajen inganta harkar rarraba iskar gas ɗin tare da nuna gaskiya a farashi domin kare haƙƙin masu amfani da shi ba tare da gurgunta gwuiwar masu zuba jari ba.
Jami’an gwamnati sun tabbatar wa mahalarta taron cewa za su ci gaba da wallafa sunayen duk wani kamfani ko mutumin da aka kama da laifin ɓoye gas ɗin, kuma za a miƙa su ga hukumomin tsaro domin fuskantar hukunci.














Discussion about this post