Tsohon Babban Mataimaki na Musamman ga Gwamnan Jihar Gombe, Aliyu Musa, ya yi murabus daga jam’iyyar APC mai mulki inda ya koma jam’iyyar PDP tare da ɗimbin magoya bayansa. Wannan sauyin sheƙa, wanda aka gudanar a lokacin wani taro na musamman a Karamar Hukumar Billiri, ana kallonsa a matsayin gagarumin sauyi ga fagen siyasar jihar gabanin zaɓen gwamna na shekarar 2027.
Aliyu Musa ya bayyana cewa ya ɗauki wannan mataki ne domin marawa tsohon Ministan Sadarwa da Tattalin Arziki na Zamani, Isa Ali Ibrahim Pantami baya, wanda ya fito takarar gwamna a ƙarƙashin inuwar PDP. Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya ne ya naɗa Musa a matsayin mataimaki na musamman kan harkokin siyasa tun a watan Mayun shekarar 2025 kafin daga bisani ya ajiye aikin nasa.
Waɗanda suka shirya taron sun bayyana cewa sama da maza da mata 1,800 ne daga yankin Billiri suka bar jam’iyyun APC da Labour Party domin komawa PDP saboda mutunta takarar ta Pantami. Masana siyasa na ganin cewa wannan sauyin sheka zai ƙara ƙarfafa gwuiwar jam’iyyar PDP a shiyyar Gombe ta Kudu, musamman a Billiri, a daidai lokacin da jam’iyyu ke zafafa kamfen.
Pantami ya fita ne daga APC ne bayan wani saɓani da aka samu kan tsarin zaben fidda gwani, inda ya zama ɗan takara tilo a PDP tun a watan Mayu. Ya lashi takobin gudanar da gwamnati ta haɗaka da za ta mayar da hankali kan yaƙi da talauci, da inganta ilimi, da noma, da kuma fannin masana’antu idan har aka zaɓe shi a matsayin gwamna.














Discussion about this post