ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kungiyar Jama’atu Ta Yi Tir Da Kashe-kashen Da Suka Auku A Jos

by Sani Anwar and Sulaiman
5 months ago
Jos

Kungiyar Jama’atu Nasril Islam (JNI), reshen Jihar Filato, ta bayyana hare-haren da aka kai wa al’ummar unguwar Rukuba da ke Karamar Hukumar Jos ta Arewa, a matsayin na dabbanci da rashin hankali, inda ta yi kira ga gwamnati da hukumomin da abin ya shafa da su gaggauta yin bincike a kan wadanda suka haddasa lamarin.

Shaidun gani da ido a ranar Lahadin da ta gabata, sun bayyana cewa; maharan wadanda suka yi amfani da babura, sun mamaye al’ummar ne da misalin karfe 7:30 na dare, a daidai lokacin da jama’a ke gudanar da harkokinsu na yau da kullum, inda suka fara harbe-harbe babu gaira babu dalili, lamarin da ya haifar da firgici a tsakanin mazauna yankin.

  • Fadar Shugaban Ƙasa Ta Soki Jami’iyyar ADC, Ta Ce Su Fuskanci Matsalolinsu
  • Mutane Da Dama Sun Jikkata A Rikicin ‘Yan Daba A Kano

Rundunar ‘yansandan Jihar Filato, ta tabbatar da kashe mutum 14 da suka hada da mata biyu, amma shugaban kungiyar matasan Berom na kasa (BYM), Barista Solomon Dalyop, ya yi ikirarin kashe mutum 27.

ADVERTISEMENT

JNI, a cikin wata sanarwa dauke da sa hannun sakatarenta, Dr. Salim Musa Umar, ta bayyana matukar kaduwarta tare da alhinin faruwar lamarin, wanda ya yi sanadiyyar asarar rayuka da dama tare da yin kakkausar suka ga harin.

Haka zalika, ta bayyana harin a matsayin na dabbanci da rashin hankali, inda ta ce; babbar barazana ce ga zaman lafiya a jihar ta Filato.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

Sanarwar ta ce, “Muna matukar bakin ciki da faruwar wannan bala’i, sannan kuma bai kamata a taba keta alfarmar rayuwar Bil’adama ba a kowane hali, wannan ta’addancin ba abu ne da za a amince da shi ba, kuma wajibi ne kowa ya yi Allah-wadai da shi.”

Dakta Salim ya kuma mika ta’aziyya ga iyalan wadanda suka rasu tare da yin addu’ar Allah ya ji kan wadanda suka rasu, tare da yi wa wadanda suka jikkata fatan samun sauki cikin gaggawa.

Kungiyar ta kuma yi kira ga al’ummar jihar, da su kwantar da hankalinsu tare da bin doka da oda, tare da gargadin duk wani nau’in ramuwar gayya da ka iya kara ruruta wutar rikici.

JNI ta kara da cewa, “A wannan mawuyacin lokaci, muna kira ga dukkan ‘yan kasa, da su kasance masu kamun kai, kada mu bar fushi da bakin ciki su sa mu shiga aikata ayyukan da za su iya dagula mana al’amuranmu.”

Haka kuma, ta yi kira ga hukumomin tsaro da su gaggauta gudanar da cikakken bincike na gaskiya da adalci kan lamarin, da nufin zakulo wadanda suka aikata laifin da kuma gurfanar da su a gaban kuliya.

JNI ta jaddada kudirinta na inganta zaman lafiya da hadin kai da adalci a Jihar Filato da ma Nijeriya baki-daya.

Jos
Sani Anwar
+ posts Bio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Ko Kun San Amfanin Kwanciya Da Bangaren Hagu?
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    2027:Mata Shida Da Ke Takarar Neman Shugabancin Nijeriya
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Dambarwa A Kasuwancin Iyalan Indimi
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Illar Shan Taba Sigari Da Dangoginta
Jos
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • Sulaiman
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • Sulaiman
    ‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna
  • Sulaiman
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

MASU ALAKA

'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina
Labarai

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare
Labarai

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Next Post
Kungiyar SSANU Ta Nemi Gwamnatin Tarayya Ta Mutunta Yarjejeniyarsu Ta 2009

Kungiyar SSANU Ta Nemi Gwamnatin Tarayya Ta Mutunta Yarjejeniyarsu Ta 2009

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.