ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 14, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kungiyar Jama’atu Ta Yi Tir Da Kashe-kashen Da Suka Auku A Jos

by Sani Anwar and Sulaiman
3 months ago
Jos

Kungiyar Jama’atu Nasril Islam (JNI), reshen Jihar Filato, ta bayyana hare-haren da aka kai wa al’ummar unguwar Rukuba da ke Karamar Hukumar Jos ta Arewa, a matsayin na dabbanci da rashin hankali, inda ta yi kira ga gwamnati da hukumomin da abin ya shafa da su gaggauta yin bincike a kan wadanda suka haddasa lamarin.

Shaidun gani da ido a ranar Lahadin da ta gabata, sun bayyana cewa; maharan wadanda suka yi amfani da babura, sun mamaye al’ummar ne da misalin karfe 7:30 na dare, a daidai lokacin da jama’a ke gudanar da harkokinsu na yau da kullum, inda suka fara harbe-harbe babu gaira babu dalili, lamarin da ya haifar da firgici a tsakanin mazauna yankin.

  • Fadar Shugaban Ƙasa Ta Soki Jami’iyyar ADC, Ta Ce Su Fuskanci Matsalolinsu
  • Mutane Da Dama Sun Jikkata A Rikicin ‘Yan Daba A Kano

Rundunar ‘yansandan Jihar Filato, ta tabbatar da kashe mutum 14 da suka hada da mata biyu, amma shugaban kungiyar matasan Berom na kasa (BYM), Barista Solomon Dalyop, ya yi ikirarin kashe mutum 27.

ADVERTISEMENT

JNI, a cikin wata sanarwa dauke da sa hannun sakatarenta, Dr. Salim Musa Umar, ta bayyana matukar kaduwarta tare da alhinin faruwar lamarin, wanda ya yi sanadiyyar asarar rayuka da dama tare da yin kakkausar suka ga harin.

Haka zalika, ta bayyana harin a matsayin na dabbanci da rashin hankali, inda ta ce; babbar barazana ce ga zaman lafiya a jihar ta Filato.

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

Sojoji Sun Daƙile Harin ISWAP A Borno

Sanarwar ta ce, “Muna matukar bakin ciki da faruwar wannan bala’i, sannan kuma bai kamata a taba keta alfarmar rayuwar Bil’adama ba a kowane hali, wannan ta’addancin ba abu ne da za a amince da shi ba, kuma wajibi ne kowa ya yi Allah-wadai da shi.”

Dakta Salim ya kuma mika ta’aziyya ga iyalan wadanda suka rasu tare da yin addu’ar Allah ya ji kan wadanda suka rasu, tare da yi wa wadanda suka jikkata fatan samun sauki cikin gaggawa.

Kungiyar ta kuma yi kira ga al’ummar jihar, da su kwantar da hankalinsu tare da bin doka da oda, tare da gargadin duk wani nau’in ramuwar gayya da ka iya kara ruruta wutar rikici.

JNI ta kara da cewa, “A wannan mawuyacin lokaci, muna kira ga dukkan ‘yan kasa, da su kasance masu kamun kai, kada mu bar fushi da bakin ciki su sa mu shiga aikata ayyukan da za su iya dagula mana al’amuranmu.”

Haka kuma, ta yi kira ga hukumomin tsaro da su gaggauta gudanar da cikakken bincike na gaskiya da adalci kan lamarin, da nufin zakulo wadanda suka aikata laifin da kuma gurfanar da su a gaban kuliya.

JNI ta jaddada kudirinta na inganta zaman lafiya da hadin kai da adalci a Jihar Filato da ma Nijeriya baki-daya.

Jos
Sani Anwar
+ posts Bio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Shugaban Rundunar Sojojin Nijeriya Ya Nemi Haɗin Kan Fararen Hula
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Ƴan Ƙwadago Sun Buƙaci Naira 300,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    NiMet Ta Gargaɗi Jihohi 27 Kan Barazanar Ambaliyar Ruwa A Farkon Watan Yuli
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Amince Da Jamilu Gwamna A Matsayin Gwamnan Gombe
Jos
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai
  • Sulaiman
    Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC
  • Sulaiman
    Tsaka mai wuyar Infantino da Koma bayan mulkin yamma
  • Sulaiman
    Abin Da Ake Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin” Da Aka Yanke Wa Sin Na Kashin Kanta Ba Shi Da Wani Amfani

MASU ALAKA

Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC
Manyan Labarai

Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

July 14, 2026
Sojoji Sun Kashe ’Yan Ta’adda 3, Sun Ƙwato Makamai A Sakkwato
Manyan Labarai

Sojoji Sun Daƙile Harin ISWAP A Borno

July 14, 2026
Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya
Rahotonni

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

July 14, 2026
Next Post
Kungiyar SSANU Ta Nemi Gwamnatin Tarayya Ta Mutunta Yarjejeniyarsu Ta 2009

Kungiyar SSANU Ta Nemi Gwamnatin Tarayya Ta Mutunta Yarjejeniyarsu Ta 2009

LABARAI MASU NASABA

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026
Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

July 14, 2026
ADC Ta Nemi A Binciki Nafiu Bala Bayan INEC Ta Ƙaryata Iƙirarinsa

ADC Ta Nemi A Binciki Nafiu Bala Bayan INEC Ta Ƙaryata Iƙirarinsa

July 14, 2026
Sojoji Sun Kashe ’Yan Ta’adda 3, Sun Ƙwato Makamai A Sakkwato

Sojoji Sun Daƙile Harin ISWAP A Borno

July 14, 2026
Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

July 14, 2026
Tsaka mai wuyar Infantino da Koma bayan mulkin yamma

Tsaka mai wuyar Infantino da Koma bayan mulkin yamma

July 14, 2026
“Buhari Ya Taɓa tambaya Ta Mutane Nawa Na Kashe Saboda Yawan Azumin Dana Ke Yi”

“Buhari Ya Taɓa tambaya Ta Mutane Nawa Na Kashe Saboda Yawan Azumin Dana Ke Yi”

July 14, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Ce Za A Gurfanar Da Tubabbun ’Yan ta’addan Da Suka Sake Aikata Manyan Laifuka

Gwamnatin Tarayya Ta Ce Za A Gurfanar Da Tubabbun ’Yan ta’addan Da Suka Sake Aikata Manyan Laifuka

July 14, 2026
Tinubu Ya Gana da Gwamnan Kwara Bayan Harin Ta’addanci Da Ya Yi Ajalin Sama Da Mutane 160

Kyawawan Manufofin Buhari Za Su Ci Gaba Da Yi Wa ’Yan Nijeriya Tasiri – Tinubu

July 14, 2026
Abin Da Ake Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin” Da Aka Yanke Wa Sin Na Kashin Kanta Ba Shi Da Wani Amfani

Abin Da Ake Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin” Da Aka Yanke Wa Sin Na Kashin Kanta Ba Shi Da Wani Amfani

July 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.