ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kungiyar Jama’atu Ta Yi Tir Da Kashe-kashen Da Suka Auku A Jos

by Sani Anwar and Sulaiman
3 months ago
Jos

Kungiyar Jama’atu Nasril Islam (JNI), reshen Jihar Filato, ta bayyana hare-haren da aka kai wa al’ummar unguwar Rukuba da ke Karamar Hukumar Jos ta Arewa, a matsayin na dabbanci da rashin hankali, inda ta yi kira ga gwamnati da hukumomin da abin ya shafa da su gaggauta yin bincike a kan wadanda suka haddasa lamarin.

Shaidun gani da ido a ranar Lahadin da ta gabata, sun bayyana cewa; maharan wadanda suka yi amfani da babura, sun mamaye al’ummar ne da misalin karfe 7:30 na dare, a daidai lokacin da jama’a ke gudanar da harkokinsu na yau da kullum, inda suka fara harbe-harbe babu gaira babu dalili, lamarin da ya haifar da firgici a tsakanin mazauna yankin.

  • Fadar Shugaban Ƙasa Ta Soki Jami’iyyar ADC, Ta Ce Su Fuskanci Matsalolinsu
  • Mutane Da Dama Sun Jikkata A Rikicin ‘Yan Daba A Kano

Rundunar ‘yansandan Jihar Filato, ta tabbatar da kashe mutum 14 da suka hada da mata biyu, amma shugaban kungiyar matasan Berom na kasa (BYM), Barista Solomon Dalyop, ya yi ikirarin kashe mutum 27.

ADVERTISEMENT

JNI, a cikin wata sanarwa dauke da sa hannun sakatarenta, Dr. Salim Musa Umar, ta bayyana matukar kaduwarta tare da alhinin faruwar lamarin, wanda ya yi sanadiyyar asarar rayuka da dama tare da yin kakkausar suka ga harin.

Haka zalika, ta bayyana harin a matsayin na dabbanci da rashin hankali, inda ta ce; babbar barazana ce ga zaman lafiya a jihar ta Filato.

LABARAI MASU NASABA

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sanarwar ta ce, “Muna matukar bakin ciki da faruwar wannan bala’i, sannan kuma bai kamata a taba keta alfarmar rayuwar Bil’adama ba a kowane hali, wannan ta’addancin ba abu ne da za a amince da shi ba, kuma wajibi ne kowa ya yi Allah-wadai da shi.”

Dakta Salim ya kuma mika ta’aziyya ga iyalan wadanda suka rasu tare da yin addu’ar Allah ya ji kan wadanda suka rasu, tare da yi wa wadanda suka jikkata fatan samun sauki cikin gaggawa.

Kungiyar ta kuma yi kira ga al’ummar jihar, da su kwantar da hankalinsu tare da bin doka da oda, tare da gargadin duk wani nau’in ramuwar gayya da ka iya kara ruruta wutar rikici.

JNI ta kara da cewa, “A wannan mawuyacin lokaci, muna kira ga dukkan ‘yan kasa, da su kasance masu kamun kai, kada mu bar fushi da bakin ciki su sa mu shiga aikata ayyukan da za su iya dagula mana al’amuranmu.”

Haka kuma, ta yi kira ga hukumomin tsaro da su gaggauta gudanar da cikakken bincike na gaskiya da adalci kan lamarin, da nufin zakulo wadanda suka aikata laifin da kuma gurfanar da su a gaban kuliya.

JNI ta jaddada kudirinta na inganta zaman lafiya da hadin kai da adalci a Jihar Filato da ma Nijeriya baki-daya.

Jos
Sani Anwar
+ posts Bio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Tattalin Arziƙin Ƙasa: Masana Sun Buƙaci Tinubu Ya Yi Hattara Da Shawarar IMF
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (2)
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF
Jos
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu
  • Sulaiman
    Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani
  • Sulaiman
    Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100
  • Sulaiman
    Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

MASU ALAKA

‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba
Labarai

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi
Labarai

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Next Post
Kungiyar SSANU Ta Nemi Gwamnatin Tarayya Ta Mutunta Yarjejeniyarsu Ta 2009

Kungiyar SSANU Ta Nemi Gwamnatin Tarayya Ta Mutunta Yarjejeniyarsu Ta 2009

LABARAI MASU NASABA

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

’Yansanda Sun Kama Mutane 57 Da Ake Zargi Da Ayyukan Ta’addanci A Adamawa

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.