Kungiyar wayar da kan mabiyan darikar Tijjaniyya da tallafawa al’umma ta Nijeriya (TIGMEIN) tare da wasu sun bukaci Gwamnatin tarayya da ta gaggauta sakin malamin addinin musulunci Sheikh Sani Khalifa Zaria, suna mai bayyana ci gaba da tsare shi a matsayin take hakkin dan Adam da kuma karya kundin tsarin mulki.
Kungiyar ta bayyana hakan ne yayin wani taron manema labarai da aka gudanar a hedikwatar TIGMEIN da ke Kaduna karkashin jagorancin shugabanta Sayyadi Nasiru Sheikh Bello (Hayin Banki)Shugaban , yace an shafe watanni ana tsare da Sheikh Sani Khalifa Zaria ba tare da gabatar da shi gaban kotu cikin adalci ko bayyana hujjar da ta dace ba, lamarin da suka ce ya saɓa wa sashe na 35 da 36 na kundin tsarin mulkin Najeriya na shekarar 1999 wanda ya tanadi ‘yancin walwala da sauraron karar kowa cikin adalci.
Kungiyar ta bayyana cewa babbar Kotun tarayya ta riga ta yanke hukuncin cewa, ci gaba da tsare malamin ya saba wa hakkokinsa na asali, tare da umartar a sake shi ba tare da wani sharadi ba.
Haka kuma kotun ta bayar da umarnin a biya shi diyya saboda hana shi amfani da asusun ajiyarsa da kuma tsare shi ba bisa ka’ida ba.Don haka, kungiyar ta zargi Gwamnatin tarayya da kin cikakken bin umarnin kotun, inda ta ce maimakon sakin malamin, gwamnati ta sake shigar da wasu sabbin tuhume-tuhume a kansa bayan hukuncin kotun.
Kungiyar ta kuma bayyana hakan a matsayin cin zarafin tsarin shari’a da kuma barazana ga doka da oda a kasar nan.















Discussion about this post