Ministan bunkasa ma’adanai da albarkatun kasa na kasar Zambia, Paul Kabuswe, ya yaba wa kamfanonin kasar Sin saboda kawo fasahohi na zamani domin kara inganci da habaka ayyuka a sashen hakar ma’adanai na kasar.Yayin da yake jawabi a wajen kaddamar da wata na’urar hako ma’adanai a karkashin kasa ta kamfanin kasar Sin mai suna NFC Africa Mining Plc, a gundumar Kalulushi da ke lardin Copperbelt, ranar Jumma’ar da ta gabata, Kabuswe ya ce na’urar ta sabuwar fasaha tana nuna babban sauyi daga tsohuwar hanyar hakar ma’adanai ta hakowa da fashewa zuwa sabuwar fasaha ta zamani.Ya ce an kawo wannan na’urar ta hako ma’adanai a karkashin kasa mai iya juyawa a cikin kankanin wuri a kan lokacin da ya dace, domin za ta rage hayaniya da tsananin damuwar da ke tattare da fashe-fashe, sannan za ta taimaka wajen hana lalacewar kayayyakin more rayuwa.Ministan ya kuma yaba wa kamfanin na kasar Sin kan matakin da ya dauka na kara zuba jari a Zambia, yana mai cewa wannan jarin ba wai kawai zai kara yawan samarwa ba ne, har ma zai samar da sabbin ayyukan yi. (Mai fassara: Abdulrazaq Yahuza Jere)















Discussion about this post