Fitaccen malamin addinin Musulunci da ke Kaduna, Sheikh Ahmad Gumi, ya nesanta kansa daga kalaman da ke danganta shi da goyon bayan ayyukan ’yan bindiga, yana mai bayyana irin waɗannan zarge-zarge a matsayin ƙarya da aka ƙirƙira domin bata masa suna.
A cikin wata sanarwa da ya fitar ranar Asabar, malamin ya ce ya lura ana karkatar da kalamansa a hirarrakin kafafen yaɗa labarai da kuma jawabansa kan hanyoyin magance matsalar tsaro da ’yan bindiga a Nijeriya.
“Na lura cewa ana jirkita da kalamaina daga hirarrakin kafafen yaɗa labarai da kuma jawabaina kan yadda za a magance matsalar ’yan bindiga a Nijeriya,” in ji Sheikh Ahmad Gumi. Ya zargi wasu mutane da masu ƙirƙirar bayanai a intanet da amfani da kanun labarai masu tayar da hankali domin neman masu kallo.
Malamin ya jaddada cewa duk wani bidiyo, ko rubutu ko saƙon da ake danganta masa da goyon baya ko kare ayyukan ’yan bindiga ba daga gare shi suka fito da su ba. Haka kuma ya buƙaci jama’a, kafafen yaɗa labarai da hukumomi da su yi watsi da duk wasu bayanai da aka jirkita ko ƙirƙira da sunansa.
Sheikh Ahmad Gumi ya kuma yi gargaɗin cewa duk wanda ya ci gaba da yaɗa ƙarya a kansa bayan wannan sanarwa zai iya fuskantar matakin shari’a. Ya ƙara da fatan Nijeriya za ta samu mafita daga matsalar tsaro tare da kira ga haɗin kai wajen tallafa wa waɗanda rikici ya shafa.















Discussion about this post