Kwamandan Rundunar Sojojin Ƙasa ta Nijeriya, Manjo Janar Godwin Mutkut, ya umarci dakarun Hedikwatar Birget ta 27 na Rundunar Haɗin Gwiwa ta ‘Operation HADIN KAI’, Shiyya 2, da su ci gaba da nuna jajircewa, ƙwarewa da ƙara matsin lamba a yaƙin da ake yi da mayaƙan Boko Haram da ƙungiyar ISWAP a yankin Arewa maso Gabas.
A cikin wani saƙo da aka wallafa a shafin X ranar Laraba, Mukaddashin Mataimakin Daraktan Hulɗa da Jama’a na Birget ta 27 da ke Buni-Gari, Ƙaramar Hukumar Gujba ta Jihar Yobe, Laftanar Tasi’u Abbas, ya ce Mutkut ya bayar da wannan umarni ne a ranar Talata, 28 ga Yuli, 2026, yayin wata ziyarar tantance ayyukan rundunar a hedikwatarta.
A yayin ziyarar, kwamandan ya duba yadda ayyukan soji ke gudana tare da ganawa da manyan jami’ai da dakaru.Ya yabawa dakarun bisa jarumtaka, juriya da sadaukarwar da suke yi wajen kare martabar yankunan Nijeriya duk da ƙalubalen da suke fuskanta a fagen daga.
Da yake jawabi ga dakarun, Mutkut ya jaddada muhimmancin ci gaba da matsa wa ƙungiyoyin ta’addanci lamba, yana mai cewa hana su damar gudanar da ayyukansu cikin ‘yanci shi ne mabuɗin samun nasara a yaƙin.
Ya ce, “Ci gaba da matsa wa ‘yan ta’adda lamba a fagen daga shi ne hanya mafi inganci ta hana su samun damar gudanar da ayyukansu.”














