Kwamitin kolin jam’iyyar kwaminis ta Sin (JKS), da majalisar gudanarwar kasar sun gudanar da taron murnar bikin bazara da safiyar yau Asabar a babban dakin taron jama’a domin mika gaisuwar bikin bazara na sabuwar shekara ta 2026 ga Sinawa. Xi Jinping, babban sakataren kwamitin kolin JKS, shugaban kasar, kuma shugaban kwamitin soja, ya gabatar da jawabi, inda ya mika gaisuwar sabuwar shekara a madadin kwamitin kolin JKS da majalisar gudanarwa ga al’ummun dukkanin kabilu a fadin kasar, da kuma al’ummun yankin musamman na Hong Kong da yankin musamman na Macao da yankin Taiwan da kuma ’yan asalin Sin dake kasashen waje.
Xi Jinping ya jaddada cewa, shekarar da ta gabata ta kasance ta musamman, inda aka fuskanci yanayi mai sarkakiya da rashin tabbas a kasa da kasa, amma an kammala manyan ayyukan raya tattalin arziki da zamantakewa cikin nasara, kuma an dauki sabbin matakai masu inganci kan zamanantarwa iri ta kasar Sin.
Ya kara da cewa shekarar 2026 ita ce ta cika shekaru 105 da kafuwar jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin. Ya ce ya kamata dukkan sassa su bi jagorancin ra’ayin gurguzu irin na kasar Sin a sabon zamani, su hanzarta gina sabon tsarin ci gaba, su mai da hankali kan inganta ci gaba mai inganci, su kiyaye jituwa da kwanciyar hankalin zamantakewa, kuma su dage wajen tafiyar da shugabancin jam’iyyar, ta yadda za a yi kokarin cimma kyakkyawan mafari yayin aiwatar da shirin raya kasa na shekaru biyar-biyar karo na 15.(Safiyah Ma)














