Biyo bayan jawabin da Shugaban kasa Ahmed Bola Tinubu ya gabatar da taro karo na biyu na majalisar tattalin arzikin kasa wato NEC, Mataimakin Shugaban kasar Sanata Kashim Shettima, ya bukaci daukacin gwamonin jihohin kasar 36, da su taimaka kan kokarin da Gwamnatin Tarayya ke ci gaba da yi, na kara habaka fannin tattalin arzikin kasar.
Kazalika, Shettima, ya kuma kara gabatar da irin wannan bukatar, ga ministoci da jami’an gwamnati, wajen ganin an cimma wannan burin.
- Hukumar Zabe Ta Yi Kadan Ta Zaba Wa Jam’iyyar PDP Shugabanni – Turaki
- Sin Ta Nuna Karfinta Na Sarrafa Bayanai Bisa Amfani Da Fasahar AI A Sararin Samaniya
Ya yi nuni da yin hakan zai kara taimaka wa, wajen kara inganta rayuwa da kuma tattalin arzikin ‘yan kasar..
A cewarsa, kasashen da suka ci gaba wajen habaka tattalin arzikinsu, batun na su, ya wuce maganar habaka tattalin arzikinsu, har da kan yadda za su ingnata rayuwar ‘yan kasar su.
Ya yi wannan kiran ne, a taron da majalisar ta gudanar a fadar shugaban kasa da ke a babban birnin tarayyar Abuja.
Ya kara da cewa, zaman na kwana biyu, tamkar wani babi na ci gaba da kuma kokarin aiwatar da yarjejeniyar gwamnati da ‘yan kasar nan.
Kazalika, ya jinjinawa kokarin da shugaban kasar ke ci gaba da yi, na kara inganta fannin tattalin arzikin kasar, musammankan sauye-sauyen da gwamnatinsa, ta kirkiro da su, na kara ciyar da kasar gaba.
Buku da kari, ya ambati wasu daga cikin manufofin da gwamnatin ta cimma, a wannan fannin, musamman domin gwamnatin tarayya, ta cimma, burin da ta sanya a gaba, musamman wadanda suka hada da, hada da kasuwanci tsakanin shiyyoyin da ke a kasar nan, a bangaren zuba hannun jari da kara samarwa da ‘yan Nijeriya, kayan more rayuwa da sauransu.















Discussion about this post