ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kwankwaso: ADC Ta Zargi Shirin Rikita Jam’iyyar, Ta Zargi Gwamnati Da Matsa Wa INEC Lamba

by Sulaiman
5 months ago
ADC

Jam’iyyar ADC ta zargi Gwamnatin Tarayya karkashin jagorancin jam’iyyar APC da kokarin haddasa rikici a cikin jam’iyyar, bayan sauya sheƙar Rabiu Musa Kwankwaso zuwa ADC.

 

A cikin wata sanarwa da Sakataren Yada Labarai na Kasa, Bolaji Abdullahi, ya sanya wa hannu, jam’iyyar ta ce ana kara matsa wa shugaban Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC), Joash Ojo Amupitan, lamba domin ya tsoma baki cikin tsarin shugabancin cikin gida na jam’iyyar.

ADVERTISEMENT
  • Alkaluman PMI Na Sin Sun Karu Da Kaso 50.4 Bisa Dari A Watan Maris
  • ‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Wajen Biki A Kaduna, Sun Kashe Mutane 13

ADC ta kuma yi zargin cewa wata wasika mai dauke da kwanan wata 28 ga Maris, 2026, da wasu manyan lauyoyi, SAN suka rubuta a madadin wani mutum da ta bayyana a matsayin tsohon mamba da aka kora, ana amfani da wannan ikirarin wajen matsa wa INEC lamba domin ta soke wasu muhimman matakai da shugabancin jam’iyyar ya dauka.

 

LABARAI MASU NASABA

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue

A cewar jam’iyyar, wasikar na kokarin tilasta wa hukumar zaben, fassara hukuncin Kotun Daukaka Kara ta yadda za a sauya tsarin jam’iyyar kafin kotu ta yanke hukunci na karshe kan lamarin.

 

Har ila yau, ADC ta yi zargin cewa wasikar ta kunshi barazana ga shugaban INEC tare da bukatar a janye wasu matakan jam’iyyar, ciki har da amincewa da wasu jami’ai.

 

Jam’iyyar ta karyata ikirarin Nafiu Bala Gombe, inda ta bayyana shi a matsayin tsohon mamba wanda ya yi murabus sannan daga bisani aka kore shi, tana mai cewa bai taba zama shugaban jam’iyyar na kasa ba.

 

Haka kuma, ADC ta danganta wannan lamari da abin da ta kira matsin lamba na siyasa bayan sauya sheƙar Kwankwaso kwanan nan, wanda ta ce ya kara wa jam’iyyar farin jini da goyon baya.

 

A karshe, jam’iyyar ta bukaci INEC da ta kasance mai tsaka-tsaki tare da bin tanade-tanaden kundin tsarin mulki, tana gargadin kada a yi yunkurin tsoma baki cikin harkokin cikin gida na jam’iyyar.

ADC
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • Sulaiman
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • Sulaiman
    ‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna
  • Sulaiman
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

MASU ALAKA

Ballon D'or
Manyan Labarai

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

September 8, 2026
Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue
Manyan Labarai

Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue

September 8, 2026
2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi
Manyan Labarai

2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi

September 8, 2026
Next Post
Sin Na Da Burin Habaka Masana’antar Iot Har Ta Haura Yuan Tiriliyan 3.5 Zuwa 2028

Sin Na Da Burin Habaka Masana’antar Iot Har Ta Haura Yuan Tiriliyan 3.5 Zuwa 2028

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.