ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, June 8, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kwankwaso: ADC Ta Zargi Shirin Rikita Jam’iyyar, Ta Zargi Gwamnati Da Matsa Wa INEC Lamba

by Sulaiman
2 months ago
ADC

Jam’iyyar ADC ta zargi Gwamnatin Tarayya karkashin jagorancin jam’iyyar APC da kokarin haddasa rikici a cikin jam’iyyar, bayan sauya sheƙar Rabiu Musa Kwankwaso zuwa ADC.

 

A cikin wata sanarwa da Sakataren Yada Labarai na Kasa, Bolaji Abdullahi, ya sanya wa hannu, jam’iyyar ta ce ana kara matsa wa shugaban Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC), Joash Ojo Amupitan, lamba domin ya tsoma baki cikin tsarin shugabancin cikin gida na jam’iyyar.

ADVERTISEMENT
  • Alkaluman PMI Na Sin Sun Karu Da Kaso 50.4 Bisa Dari A Watan Maris
  • ‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Wajen Biki A Kaduna, Sun Kashe Mutane 13

ADC ta kuma yi zargin cewa wata wasika mai dauke da kwanan wata 28 ga Maris, 2026, da wasu manyan lauyoyi, SAN suka rubuta a madadin wani mutum da ta bayyana a matsayin tsohon mamba da aka kora, ana amfani da wannan ikirarin wajen matsa wa INEC lamba domin ta soke wasu muhimman matakai da shugabancin jam’iyyar ya dauka.

 

LABARAI MASU NASABA

’Yan Bindiga Sun Sace Dattawan Zamfara 50 Yayin Taron Sulhu A Cikin Daji

Gwamnatin Tarayya Zata Biya Naira Biliyan 700 Ga Ƴan Kwangila 1,240 Da Aka Tantance

A cewar jam’iyyar, wasikar na kokarin tilasta wa hukumar zaben, fassara hukuncin Kotun Daukaka Kara ta yadda za a sauya tsarin jam’iyyar kafin kotu ta yanke hukunci na karshe kan lamarin.

 

Har ila yau, ADC ta yi zargin cewa wasikar ta kunshi barazana ga shugaban INEC tare da bukatar a janye wasu matakan jam’iyyar, ciki har da amincewa da wasu jami’ai.

 

Jam’iyyar ta karyata ikirarin Nafiu Bala Gombe, inda ta bayyana shi a matsayin tsohon mamba wanda ya yi murabus sannan daga bisani aka kore shi, tana mai cewa bai taba zama shugaban jam’iyyar na kasa ba.

 

Haka kuma, ADC ta danganta wannan lamari da abin da ta kira matsin lamba na siyasa bayan sauya sheƙar Kwankwaso kwanan nan, wanda ta ce ya kara wa jam’iyyar farin jini da goyon baya.

 

A karshe, jam’iyyar ta bukaci INEC da ta kasance mai tsaka-tsaki tare da bin tanade-tanaden kundin tsarin mulki, tana gargadin kada a yi yunkurin tsoma baki cikin harkokin cikin gida na jam’iyyar.

ADC
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    ’Yan Bindiga Sun Sace Dattawan Zamfara 50 Yayin Taron Sulhu A Cikin Daji
  • Sulaiman
    Xi Jinping Ya Tattauna Da Kim Jong Un
  • Sulaiman
    Yari Ya Dace Da Rayuwar Mulki Da Kasuwanci
  • Sulaiman
    Me Kashim Imam Ke Yi A Yanzu?

MASU ALAKA

Zamfara
Manyan Labarai

’Yan Bindiga Sun Sace Dattawan Zamfara 50 Yayin Taron Sulhu A Cikin Daji

June 8, 2026
Gwamnatin Tarayya Zata Biya Naira Biliyan 700 Ga Ƴan Kwangila 1,240 Da Aka Tantance
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Zata Biya Naira Biliyan 700 Ga Ƴan Kwangila 1,240 Da Aka Tantance

June 8, 2026
Ɗiyar Obasanjo Ta Fice Daga APC Bayan Gaza Samun Tikitin Takarar Gwamna
Manyan Labarai

Ɗiyar Obasanjo Ta Fice Daga APC Bayan Gaza Samun Tikitin Takarar Gwamna

June 8, 2026
Next Post
Sin Na Da Burin Habaka Masana’antar Iot Har Ta Haura Yuan Tiriliyan 3.5 Zuwa 2028

Sin Na Da Burin Habaka Masana’antar Iot Har Ta Haura Yuan Tiriliyan 3.5 Zuwa 2028

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Zamfara

’Yan Bindiga Sun Sace Dattawan Zamfara 50 Yayin Taron Sulhu A Cikin Daji

June 8, 2026
Xi Jinping Ya Tattauna Da Kim Jong Un

Xi Jinping Ya Tattauna Da Kim Jong Un

June 8, 2026
Yari Ya Dace Da Rayuwar Mulki Da Kasuwanci

Yari Ya Dace Da Rayuwar Mulki Da Kasuwanci

June 8, 2026
Me Kashim Imam Ke Yi A Yanzu?

Me Kashim Imam Ke Yi A Yanzu?

June 8, 2026
A Ƙarshe Jamilu Gwamna Ya Samu Babbar Dama Ta Yin Takara

A Ƙarshe Jamilu Gwamna Ya Samu Babbar Dama Ta Yin Takara

June 8, 2026
Yayin Da Dangote Ya Bayyana A Tattaunawar Neman Aiki…

Yayin Da Dangote Ya Bayyana A Tattaunawar Neman Aiki…

June 8, 2026
Morocco Na Fargabar Rashin Ƴan Wasa 2 Gabanin Karawa Da Brazil

Morocco Na Fargabar Rashin Ƴan Wasa 2 Gabanin Karawa Da Brazil

June 8, 2026
Gwamnatin Tarayya Zata Biya Naira Biliyan 700 Ga Ƴan Kwangila 1,240 Da Aka Tantance

Gwamnatin Tarayya Zata Biya Naira Biliyan 700 Ga Ƴan Kwangila 1,240 Da Aka Tantance

June 8, 2026
Ɗiyar Obasanjo Ta Fice Daga APC Bayan Gaza Samun Tikitin Takarar Gwamna

Ɗiyar Obasanjo Ta Fice Daga APC Bayan Gaza Samun Tikitin Takarar Gwamna

June 8, 2026
Kwamitin Majalisa Ya Kwato Naira Miliyan 521.76 Na VAT Daga CBN

Kwamitin Majalisa Ya Kwato Naira Miliyan 521.76 Na VAT Daga CBN

June 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.