ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 17, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Wajen Biki A Kaduna, Sun Kashe Mutane 13

by Sadiq
3 months ago
Kaduna

Ana zargin ‘yan bindiga sun kai hari wajen wani biki a ƙauyen Kahir da ke ƙaramar hukumar Kagarko a Jihar Kaduna, inda suka kashe aƙalla mutane 13 tare da sace wasu.

Maharan sun kai harin ne da daddare ranar Lahadi, inda suka fara harbe-harbe a wajen bikin, lamarin da ya jefa mutane cikin firgici.

  • Taɓarɓarewar Sabis: NCC Ta Umarci Kamfanonin Sadarwa Su Biya Diyya
  • 2027: Ministocin Da Ake Tsammanin Za Su Yi Murabus Kafin Wa’adin Tinubu Na Ranar 31 ga Maris

Shaidu sun ce maharan, waɗanda ke ɗauke da manyan makamai, sun yi kusan awa ɗaya suna cin karensu ba babbaka ba tare da wani ya dakatar da su ba.

ADVERTISEMENT

Wani mazaunin yankin, Shehu Bala, ya ce ‘yan bindigar sun isa wajen da misalin ƙarfe 11:47 na dare sannan suka fara harbi.

Ya ƙara da cewa wasu mutane biyu da ya sani sun ji rauni sakamakon harin.

LABARAI MASU NASABA

Mata Ta Hallaka Mijinta Da Wuƙa Watanni Biyu Bayan Aure A Kano

Kotun Ɗaukaka Ƙara Ta Dakatar Da INEC Game Da Soke Rajistar ADC Da Wasu Jam’iyyu

An garzaya da waɗanda suka ji rauni zuwa Asibitin Kagarko, yayin da aka tura waɗanda suka fi muni zuwa manyan asibitoci a Kaduna domin samun kulawa ta musamman.

Wani jagoran al’umma ya tabbatar da cewa mutane 13 sun mutu kuma an riga an binne su.

Ya ce ana ci gaba da ƙoƙarin gano adadin mutanen da aka sace.

Haka kuma, maharan sun wawashe shaguna a yankin, inda suka kwashe kayan abinci, kayayyaki da magunguna daga wani shagon sayar da magani.

Mutane da dama sun tsere zuwa dazuka domin tsira da rayukansu.

‘Yansanda sun tabbatar da faruwar lamarin, inda suka ce suna ci gaba da bincike, ciki har da gano yawan mutanen da aka sace.

Sun kuma ce za su fitar da cikakken bayani bayan sun kammala bincike.

A halin yanzu, Mataimakiyar Gwamnan Jihar Kaduna, Dakta Hadiza Sabuwa Balarabe, ta ziyarci waɗanda suka jikkata a asibiti.

MASU ALAKA

‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi
Manyan Labarai

Mata Ta Hallaka Mijinta Da Wuƙa Watanni Biyu Bayan Aure A Kano

June 17, 2026
Kotun Ɗaukaka Ƙara Ta Dakatar Da INEC Game Da Soke Rajistar ADC Da Wasu Jam’iyyu
Manyan Labarai

Kotun Ɗaukaka Ƙara Ta Dakatar Da INEC Game Da Soke Rajistar ADC Da Wasu Jam’iyyu

June 16, 2026
Tinubu Ya Kaddamar Da Katafaren Gidajen Alƙalan Kotun Ɗaukaka Ƙara A Abuja
Manyan Labarai

Tinubu Ya Kaddamar Da Katafaren Gidajen Alƙalan Kotun Ɗaukaka Ƙara A Abuja

June 16, 2026
Next Post
Gwamnonin Arewa Sun Goyi Bayan Tinubu, Sun Yi Alƙawarin Yin Aiki Tare Don Shawo Kan Matsalar Tsaro

Gwamnonin Arewa Sun Goyi Bayan Tinubu, Sun Yi Alƙawarin Yin Aiki Tare Don Shawo Kan Matsalar Tsaro

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Ceto Sauran Mutane 4 Da Aka Sace Tare Da Marigayi Janar Rabe A Katsina

Sojoji Sun Ceto Sauran Mutane 4 Da Aka Sace Tare Da Marigayi Janar Rabe A Katsina

June 17, 2026
Lionel Messi: Mutum Ko Aljan

Lionel Messi: Mutum Ko Aljan

June 17, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

June 17, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

Mata Ta Hallaka Mijinta Da Wuƙa Watanni Biyu Bayan Aure A Kano

June 17, 2026
An Kaddamar Da Wani Kwas Na Horar Da Kwararru Kan Killace Kananan Makamai Na Sin Da MDD Da Afirka 

An Kaddamar Da Wani Kwas Na Horar Da Kwararru Kan Killace Kananan Makamai Na Sin Da MDD Da Afirka

June 17, 2026
An Kaddamar Da Wani Kwas Na Horar Da Kwararru Kan Killace Kananan Makamai Na Sin Da MDD Da Afirka 

An Kaddamar Da Wani Kwas Na Horar Da Kwararru Kan Killace Kananan Makamai Na Sin Da MDD Da Afirka 

June 17, 2026
Mataimakin Firaministan Sin Zai Halarci Babban Taron Shugabanni Game Da Barkewar Cutar Ebola

Mataimakin Firaministan Sin Zai Halarci Babban Taron Shugabanni Game Da Barkewar Cutar Ebola

June 16, 2026
Kotun Ɗaukaka Ƙara Ta Dakatar Da INEC Game Da Soke Rajistar ADC Da Wasu Jam’iyyu

Kotun Ɗaukaka Ƙara Ta Dakatar Da INEC Game Da Soke Rajistar ADC Da Wasu Jam’iyyu

June 16, 2026
Tattalin Arzikin Sin Ya Tafiya Cikin Kwanciyar Hankali

Tattalin Arzikin Sin Ya Tafiya Cikin Kwanciyar Hankali

June 16, 2026
Gaza

Farashin Mai Ya Faɗi Ƙasa Da Dala 80 Bayan cimma Yarjejeniyar Amurka Da Iran

June 16, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.