ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kwankwaso Ba Shi Ne Jagoran Jam’iyyarmu Ta NNPP A Kano Da Ƙasa Ba – NNPP

by Muhammad
4 months ago
Kwankwaso

Mataimakin Shugaban Jam’iyyar NNPP na ƙasa a shiyyar Arewa maso Gabas, Alhaji Sani Danmasani, ya bayyana cewa tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar a zaɓen 2023, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, ba shi ne jagoran jam’iyyar NNPP a Jihar Kano ko a matakin ƙasa baki ɗaya ba.

Danmasani ya bayyana hakan ne cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Litinin, inda ya yi karin haske kan matsayar jam’iyyar dangane da rikicin shugabanci da NNPP ke fuskanta a ‘yan kwanakin nan.

  • Jaridar THE SUN Ta Karrama Gwamnan Zamfara Da Lambar Yabo Ta ‘Gwamnan Shekarar 2025’
  • Kwankwaso Bai Taɓa Neman Kujerar Mataimakin Shugaban Ƙasa Ba – NNPP

A cewarsa, shugabanci halastacce na NNPP yana hannun Dr. Boniface Aniebonam, wanda shi ne Shugaban Kwamitin Amintattu (BoT) na jam’iyyar, tare da Kwamitin Gudanarwa na Ƙasa, ƙarƙashin jagorancin Dr. Agbo Major.

ADVERTISEMENT

Ya bayyana matuƙar damuwa da yadda wasu kafafen yaɗa labarai ke ci gaba da bayyana Kwankwaso a matsayin jagoran NNPP, duk da cewa, a cewarsa, an kore shi daga jam’iyyar bisa zargin aikata ayyukan da suka saɓa wa dokokin jam’iyya. Danmasani ya kara da cewa kotuna da dama, ciki har da Babbar Kotun Jihar Abia da kuma Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja, sun riga sun tabbatar da korar Kwankwaso da wasu daga cikin mabiyansa daga jam’iyyar.

Danmasani ya kuma bayyana cewa Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta (INEC) ta bayar da umarni na hana Kwankwaso da tawagarsa yin hulɗa da hukumar, har sai an kammala sake bitar shari’a da ke gudana.

LABARAI MASU NASABA

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM

Ya jaddada cewa INEC ba ta da hurumin tantancewa ko naɗa jagororin jam’iyya, yana mai kira ga manema labarai da masu sharhi kan siyasa da su daina danganta Kwankwaso da matsayin jagoran NNPP, domin hakan na haifar da ruɗani ga jama’a.

A ƙarshe, Danmasani ya ce wannan bayani ya zama wajibi ne domin kare gaskiya, daidaita fahimtar jama’a, da kuma guje wa rikice-rikice, musamman a wannan lokaci da ake fuskantar sauye-sauyen siyasa gabanin babban zaɓen shekarar 2027.

Kwankwaso
Muhammad
+ postsBio
  • Muhammad
    Cikin Shekaru 28, Kudiri Ƙasa Da 10 Sanatocin Zamfara Ta Arewa Suka Gabatar A Majalisa – Shinkafi
  • Muhammad
    2027: NNPP Ta Yi Wa Korarrun Mambobinta Afuwa, Ta Yi Alƙawarin Basu Tikitin Kai-tsaye
  • Muhammad
    Musulunci Na Fuskantar Barazana A Karƙashin Mulkin Tinubu — Datti Baba-Ahmed
  • Muhammad
    Kwankwaso Tamkar Tsuntsu Ne A Siyasa Da Yake Sauya Sheƙa Daga Nan Zuwa Can – Ganduje

MASU ALAKA

Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe
Siyasa

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM
Siyasa

‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM

June 3, 2026
Gwamnatina Za Ta Mayar Da Hankali Kan Buƙatun Al’ummar Nasarawa – Wadada
Siyasa

Gwamnatina Za Ta Mayar Da Hankali Kan Buƙatun Al’ummar Nasarawa – Wadada

June 1, 2026
Next Post
Mutane 6 Sun Rasu, 23 Sun Jikkata A Hatsarin Mota A Kan Hanyar Legas–Ibadan

Mutane 6 Sun Rasu, 23 Sun Jikkata A Hatsarin Mota A Kan Hanyar Legas–Ibadan

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.