ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 18, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kyakkyawan Fata Kan Nasarar Yaki Da Akidar Mulkin Danniya A Duniya

by CGTN Hausa and Sulaiman
10 months ago
Yaki

Yau kimanin shekaru tamanin ke nan da samun gagarumar nasarar Sin a kan yakinta da maharan kasar Japan da kuma yaki kan mummunar akidar nan ta mulkin danniya, wato fascism a Turance, a fadin duniya. Yunkurin na Japan na afkawa Sin ya faro ne tun shekarar 1931, yayin da maharan na Japan suka afkawa yankin Manchuria, suka fara aiwatar da kisan kare dangi kan fararen hula ba gaira ba dalili. Daga bisani a watan Disamban shekarar 1937, suka kutsa kai a birnin Nanjing, wato babban birnin kasar Sin a wancan lokaci, inda maharan suka hallaka fararen hula da fursunonin yaki sama da dubu 300.

A bana ce dai kasar ta Sin take bikin cika shekaru 80 da samun nasara a kan maharan Japan da kuma yakin duniya kan akidar nan ta mulkin danniya.

Shekaru 14 ne sojojin na Sin suka kwashe suna gumurzu da maharan na Japan, inda daga bisani suka samu galaba a kan maharan na Japan.

ADVERTISEMENT

Wannan dai shi ne yaki mafi dadewa kuma mafi tsada a tarihin kasar Sin da sojoji suka aiwatar domin ‘yanto da ‘yan kasa.

Mutane masu hangen nesa da sanin ya kamata ne daga Sin da sauran kasashen duniya suka matsa kaimi da sadaukar da kai ba tare da sanyi a gwiwa ba, suka hada karfi da karfe wajen kawo karshen mummunar akidar nan ta mulkin danniya, abin da ya kawo sauyi mai ma’ana a tarihin karni na 20, tare da bude wani sabon babi na yin watsi da akidar yaki tare da rungumar akidar zaman lafiya.

LABARAI MASU NASABA

Daga Taklamakan Zuwa Sahara: Yadda Hamada Ke “Haifar” Da Fata

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

Alal hakika, akidar mulkin danniya akida ce wadda take tarnaki ga ci gaba da wayewa ta bil Adam, kuma yaduwar wannan akida barazana ce ga daukacin bil Adam. Don haka yaki da wannan akida ta bazu kamar wutar daji tsakanin sama da kasashe 80 daga nahiyoyin Asia, Turai, Afirka da Oceania. An kuwa tafka asarar rayukan da za su kai sama da miliyan 100, wadanda daga cikinsu sojoji da fararen hula miliyan 35 ne Sin ta yi asara.

Kasar Sin ta taka muhimmiyar rawa wajen yaki da wannan mummunar akida ta mulkin danniya, yayin da ta shiga cikin sahun sojojin sauran kasashe a yakin duniya na biyu. Kafada da kafada suka yi gumurzu wajen murkushe maharan kasashen Japan, Jamus da Italiya.

A wannan gabar, za mu fahimci cewa, samun nasarar da Sin ta yi a kan maharan na Japan da kalubalantar akidar mulkin danniya ya amfanawa sauran kasashen da suke da tunani iri daya da Sin na samar da kyakyawar makoma ga al’umma.

A yau an wayi gari ana samun sauye-sauye cikin hanzari irin wadanda ba a taba gani ba a cikin karni daya. Ana yawan samun barkewar rikici tsakanin yankuna, yayin da kuma kalubaloli a duniya suke ta kara yawaita a kullum. Don haka kamata ya yi a rinka koyon darasi daga tarihi. Ana iya shawo kan irin wadannan matsaloli ta hanyar adalci, daidaito da kuma tsarin yin garambawul a kan manufofin zamantakewa na duniya. (Lawal Mamuda)

Yaki
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Kasar Sin Ta Gabatar Da Takardar Bayani Game Da Inganta Tsarin Jagorancin Harkokin Duniya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Liu Guozhong Ya Halarci Taron Koli Kan Yadda Kasashen Afirka Za Su Fuskanci Cutar Ebola
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Myanmar
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Kasar Sin Na Samar Da Managarcin Yanayi Na Bunkasa Kirkire-kirkire Ga Masana’antun Kasa Da Kasa
Yaki
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Xi: Sin Na Gudanar Da Ayyukan Hadin Gwiwa Tsakanin Yankunan Gabashi Da Yammacin Kasar
  • Sulaiman
    Sin Ta Samar Da Tallafin Jin Kai Na Gaggawa Ga DRC Da AU
  • Sulaiman
    Fahimtar Tattalin Arzikin Sin Na Watannin Biyar Na Farkon Bana Ta Kalmomi Guda Uku
  • Sulaiman
    Kasar Sin Za Ta Habaka Bude Fannonin Hada-Hadar Kudi Ga Duniya

MASU ALAKA

Daga Taklamakan Zuwa Sahara: Yadda Hamada Ke “Haifar” Da Fata
Ra'ayi Riga

Daga Taklamakan Zuwa Sahara: Yadda Hamada Ke “Haifar” Da Fata

June 17, 2026
Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci
Ra'ayi Riga

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

June 13, 2026
Hadin Gwiwar Noma Tsakanin Sin Da Afirka: Daga “Sari Ka Ba Ni” Zuwa ” Zamanintar Da Kansu Tare”
Ra'ayi Riga

Hadin Gwiwar Noma Tsakanin Sin Da Afirka: Daga “Sari Ka Ba Ni” Zuwa ” Zamanintar Da Kansu Tare”

June 12, 2026
Next Post
Sabuwar Ajandar Mulkin Duniya Ta Nuna Alhakin Da Kasar Sin Ta Dauka

Sabuwar Ajandar Mulkin Duniya Ta Nuna Alhakin Da Kasar Sin Ta Dauka

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Ceto Mutane 5 Da Aka Sace A Kogi

Sojoji Sun Ceto Mutane 5 Da Aka Sace A Kogi

June 18, 2026
Kotu A Birtaniya Ta Wanke Diezani Daga Zargin Cin Hanci

Kotu A Birtaniya Ta Wanke Diezani Daga Zargin Cin Hanci

June 18, 2026
’Yan Bindiga Sun Kashe Mutum Ɗaya, Sun Sace Limami Da Wasu Mutane 7 A Filato

‘Yan Bindiga Sun Kashe Hakimin Gwande A Jihar Filato

June 18, 2026
Matsalar Tsaro: Davido Ya Mayar Wa Rarara Martani Kan Rashin Tsaro

Matsalar Tsaro: Davido Ya Mayar Wa Rarara Martani Kan Rashin Tsaro

June 18, 2026
Xi: Sin Na Gudanar Da Ayyukan Hadin Gwiwa Tsakanin Yankunan Gabashi Da Yammacin Kasar

Xi: Sin Na Gudanar Da Ayyukan Hadin Gwiwa Tsakanin Yankunan Gabashi Da Yammacin Kasar

June 17, 2026
Sin Ta Samar Da Tallafin Jin Kai Na Gaggawa Ga DRC Da AU

Sin Ta Samar Da Tallafin Jin Kai Na Gaggawa Ga DRC Da AU

June 17, 2026
Fahimtar Tattalin Arzikin Sin Na Watannin Biyar Na Farkon Bana Ta Kalmomi Guda Uku

Fahimtar Tattalin Arzikin Sin Na Watannin Biyar Na Farkon Bana Ta Kalmomi Guda Uku

June 17, 2026
Kasar Sin Za Ta Habaka Bude Fannonin Hada-Hadar Kudi Ga Duniya

Kasar Sin Za Ta Habaka Bude Fannonin Hada-Hadar Kudi Ga Duniya

June 17, 2026
Sin Na Gaggauta Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Kasa Da Kasa

Sin Na Gaggauta Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Kasa Da Kasa

June 17, 2026
Kasar Sin Ta Gabatar Da Takardar Bayani Game Da Inganta Tsarin Jagorancin Harkokin Duniya

Kasar Sin Ta Gabatar Da Takardar Bayani Game Da Inganta Tsarin Jagorancin Harkokin Duniya

June 17, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.