ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 7, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Manufar Cire Haraji Za Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Wajen Zamanantar Da Kansu

by Sulaiman and CGTN Hausa
2 months ago
Haraji

A ranar 3 ga wata, kwanaki biyu bayan da Sin ta fara aiwatar da manufar cire harajin kwastam gaba daya ga kasashen Afirka da ke da huldar diflomasiyya da ita, wani jirgin ruwa dauke da ton 747 na kasusuwan shanu daga Najeriya ya isa tashar jiragen ruwa ta Dayaowan da ke birnin Dalian na arewa maso gabashin Sin, wadanda suka kasance kaya na farko da aka shigo da su daga Afirka ba tare da biyan harajin kwastam ba ta tashar kwastam ta Dalian, bayan da aka fara aiwatar da sabuwar manufar cire haraji.

A ranar 1 ga watan Mayun 2026, manufar cire harajin kwastam ga kasashe 53 na Afirka masu huldar diflomasiyya da Sin ta fara aiki. Wannan mataki ya shafi kashi 100% na kayayyakin kasashen, ba tare da iyaka ko sharadi ba.

Amma me ake nufi da cire harajin kwastam ga kasashen Afirka? Hakan yana nufin cewa, an shigo da wadannan kasusuwan shanu daga Najeriya ba tare da biyan kudin kwastam na kimanin yuan 300,000 (kudin kasar Sin) ba, wanda kuma yake nufin cewa farashin tuffa daga Afirka ta Kudu zai ragu da kimanin yuan 20 a kowane akwati. Har wa yau, yana nufin cewa koko daga Cote d’Ivoire da Ghana ba za su kara biyan harajin kwastam na kimanin kashi 8% zuwa 22% ba.

ADVERTISEMENT

Kamar yadda kamfanin shigo da kayayyakin na kasusuwan shanu na kasar Sin ya bayyana, kasusuwan shanu su ne muhimmin sinadari wajen kera gelatin. Bayan aiwatar da manufar cire harajin kwastam, ana sa ran kudin da kamfanin ke biya wajen sayen kasusuwan shanu zai ragu da sama da yuan miliyan 3 a duk shekara.

Hakan zai bai wa kamfanonin Sin damar habaka sayen kayayyaki daga kasashen Afirka, yayin da masu sayayya na kasar Sin za su samu damar sayen kayayyakin Afirka masu inganci cikin rahusa. Ke nan wannan zai amfani kowane bangare.

LABARAI MASU NASABA

Mu Leka Yadda Kasar Sin Ke Raya Hakkin Dan Adam Daga Taron Gefe Na UNHRC

Ga “Itacen Kuka” Na Kasar Sin

Tun da dadewa, Afirka tana fitar da albarkatun kasa ne kawai a kasuwannin duniya. Wasu ‘yan uwanmu na Afirka na iya damuwa: Shin cire harajin kwastam yana nufin Afirka za ta ci gaba da fitar da albarkatun kasa cikin farashi mai rahusa? A hakika, manufar cire harajin kwastam tana rage farashin kayayyakin Afirka don kara samun damar shiga kasuwar Sin, a sa’i daya kuma, za ta jawo jari da fasaha daga kasa da kasa, wanda hakan zai taimaka ga inganta ayyukan sarrafa kayayyaki a gida don kara musu kima.

Ta haka ne ciniki zai taimaka wa Afirka raya sassan noma da masana’antu.

Bugu da kari, manufar cire harajin kwastam zai karfafa ma’aikatan Afirka ta hanyar ciniki, tare da inganta samar da ayyukan yi, kuma gaba daya tana baiwa kasashen Afirka damar tsayawa a kafafuwansu don raya kansu. Kamar yadda shugaban sashen koyon ilimin tattalin arziki na Jami’ar Kasa ta Lesotho, Dr. Leseko Makhetha, ya ce: “Manufar cire harajin kwastam kai tsaye tana tallafawa bunkasuwar masana’antu a Afirka, domin ba wai kawai ga albarkatun kasa ba, har ma ga kayayyakin da aka sarrafa da kayan karshe.

Manufar tana karfafa wa masana’antu na gida gwiwar habaka samar da kayayyaki, da inganta sarrafa kayayyakin da ke da karin kima, da samar da ayyukan yi a fannoni daban-daban.”A halin yanzu, tattalin arzikin duniya na fuskantar kariyar kasuwanci da kuma tashe-tashen hankula na siyasa.

Matakin cire harajin kwastam na Sin ba wai kyauta ce ta tattalin arziki ga kasashen Afirka ba, har ma da sakon siyasa mai karfi, wato yayin da tsarin kasuwancin duniya ke fuskantar matsaloli, Sin ta tsaya tsayin daka a kan bude kofarta ga kasashen Afirka, inda ta kafa sabon misali ga hadin gwiwar kasashe masu tasowa.

A shekarar 2025, yawan ciniki tsakanin Sin da Afirka ya kai dala biliyan 348, wanda ya karu da kashi 17.7%, tare da kafa sabon tarihi. Sai kuma a rubu’in farko na shekarar 2026, yawan ciniki a tsakanin sassan biyu ya karu da kashi 26.8%.

Ba shakka, manufar cire haraji za ta taimaka wa cinikin Sin da Afirka ya kai wani sabon matsayi.

Haraji
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Kasuwa Ce Ke Saita Tsarin Cinikayyar Sin Da EU In Ji Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin
  • Sulaiman
    Dukkan Kabilun Kasar Sin Na Zaman Tsintsiya Madaurinki Daya
  • Sulaiman
    Mutane 15 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Jihar Kwara
  • Sulaiman
    Gwamnatin Sin Ta Fara Aika Zagayen Farko Na Kayakin Agajin Gaggawa Ga Venezuela
Haraji
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Kasuwa Ce Ke Saita Tsarin Cinikayyar Sin Da EU In Ji Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Dukkan Kabilun Kasar Sin Na Zaman Tsintsiya Madaurinki Daya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Gwamnatin Sin Ta Fara Aika Zagayen Farko Na Kayakin Agajin Gaggawa Ga Venezuela
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    FIFA Ta Tsallake Iyakarta Dangane Da Batun Dakatarwar Balogun – UEFA

MASU ALAKA

Mu Leka Yadda Kasar Sin Ke Raya Hakkin Dan Adam Daga Taron Gefe Na UNHRC
Ra'ayi Riga

Mu Leka Yadda Kasar Sin Ke Raya Hakkin Dan Adam Daga Taron Gefe Na UNHRC

July 6, 2026
Ga “Itacen Kuka” Na Kasar Sin
Ra'ayi Riga

Ga “Itacen Kuka” Na Kasar Sin

July 1, 2026
Shekaru 105 Na Jam’iyyar Kwaminis Ta Kasar Sin: Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa Daga Kwarewar Ci Gaban Kasar Sin
Ra'ayi Riga

Shekaru 105 Na Jam’iyyar Kwaminis Ta Kasar Sin: Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa Daga Kwarewar Ci Gaban Kasar Sin

June 30, 2026
Next Post
Sanatan Kaduna Ta Arewa Ya Fice Daga PDP Ya Koma ADC

Sanatan Kaduna Ta Arewa Ya Fice Daga PDP Ya Koma ADC

LABARAI MASU NASABA

Kasuwa Ce Ke Saita Tsarin Cinikayyar Sin Da EU In Ji Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin

Kasuwa Ce Ke Saita Tsarin Cinikayyar Sin Da EU In Ji Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin

July 6, 2026
Dukkan Kabilun Kasar Sin Na Zaman Tsintsiya Madaurinki Daya

Dukkan Kabilun Kasar Sin Na Zaman Tsintsiya Madaurinki Daya

July 6, 2026
Mutane 15 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Jihar Kwara

Mutane 15 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Jihar Kwara

July 6, 2026
Gwamnatin Sin Ta Fara Aika Zagayen Farko Na Kayakin Agajin Gaggawa Ga Venezuela

Gwamnatin Sin Ta Fara Aika Zagayen Farko Na Kayakin Agajin Gaggawa Ga Venezuela

July 6, 2026
FIFA Ta Tsallake Iyakarta Dangane Da Batun Dakatarwar Balogun – UEFA

FIFA Ta Tsallake Iyakarta Dangane Da Batun Dakatarwar Balogun – UEFA

July 6, 2026
Shugabannin Sin Da Madagascar Sun Yi Musayar Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 20 Da Kulla Alakar Diflomasiyya Tsakaninsu

Shugabannin Sin Da Madagascar Sun Yi Musayar Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 20 Da Kulla Alakar Diflomasiyya Tsakaninsu

July 6, 2026
Rashin Tsaro: Kisa Ne Ya Fi Cancanta Ga ‘Yan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Ɗan Majalisa Gagdi

Rashin Tsaro: Kisa Ne Ya Fi Cancanta Ga ‘Yan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Ɗan Majalisa Gagdi

July 6, 2026
Mu Leka Yadda Kasar Sin Ke Raya Hakkin Dan Adam Daga Taron Gefe Na UNHRC

Mu Leka Yadda Kasar Sin Ke Raya Hakkin Dan Adam Daga Taron Gefe Na UNHRC

July 6, 2026
ADC Ta Rushe Shugabannin Jam’iyyar A Kano, Ta Naɗa Kwamitin Riƙo

ADC Ta Rushe Shugabannin Jam’iyyar A Kano, Ta Naɗa Kwamitin Riƙo

July 6, 2026
Rundunar Sojin Ruwan Sin Ta Yi Gwajin Makami Mai Linzami Ta Amfani Da Jirgin Ruwa Mai Nutso

Rundunar Sojin Ruwan Sin Ta Yi Gwajin Makami Mai Linzami Ta Amfani Da Jirgin Ruwa Mai Nutso

July 6, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.