Sanata Ibrahim Mustapha, wanda ke wakiltar mazaɓar Kaduna ta Arewa a Majalisar Dattawa, ya fice daga jam’iyyar PDP tare da komawa ADC.
An karanta wasiƙar ficewarsa a zauren Majalisar Dattawa a ranar Alhamis, wadda Mataimakin Shugaban Majalisar, Barau Jibrin ya karanta.
A cikin wasiƙar, Mustapha ya ce ya fice saga PDP ne saboda matsalolin shugabanci da ke ci gaba da addabar jam’iyyar.
Ya kuma ce ya yanke shawarar ne bayan tattaunawa da magoya bayansa da abokan hulɗarsa na siyasa.
Ya bayyana cewa shiga ADC zai taimaka masa wajen ci gaba da harkokin siyasarsa.
Sanatan ya gode wa PDP bisa damar da ta ba shi ya yi aiki a ƙarƙashin tutar jam’iyyar, tare da yi mata fatan alheri.















Discussion about this post