ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Manyan Kalubalen Da Ke Gaban Tinubu Gabanin Rantsar Da Shi

by Sulaiman and Yusuf Shuaibu
3 years ago
Tinubu

Yayin da ya kasnce a ranar 29 ga watan Mayu za a rantsar da zababben Shugaban kasa, Bola Tinubu akwai manyan kalubalen da suke gabansa kafin ya samu nasarar darewa kan karagar mulki.

Daga daga cikin wadannan kalubale ita ce, tsarin karba-karba wurin zaben shugabannin majalisu, wanda an dade ana kai-ruwa-rana a tsaknin mambobin zauren majalisun guda biyu na yadda ake kokarin saka addini da bangarenci ta yadda za a bai wa sashin kudu masu yamma, yayin da wasu ke ganin ya dace a bai wa yankin arewa maso yamma matsayin, saboda yawan kuri’u da zababben shugaban kasa ya samu a wannan yanki.

  • Lafiyata Kalau, Na Shirya Tsaf Don Shugabantar Nijeriya —Tinubu

Haka kuma sababbin mambobin majalisa idanuwansu na kan samun zama shugaban majalisan dattawa, saboda yadda aka zabe su a matsayin ‘yan majalisa a yankunan arewa da kuma na kudu, inda yankin kudu maso gabas ya koko kan yadda bai taba rike wannan kujarar ba. Ana ganin yankin kudu maso kudu ke rige-rige da yankin kudu maso gabas wajen samun mukamin shugabancin majalisan dattawa, domin tabbatar da kirista ya zamanshugaban majalisan dattawa ta yadda za a samu daidaito a tsakanin addinai lasancewa takarar musulmi da musulmi jam’iyyar APC ta yi.

ADVERTISEMENT

Samun shugaban majalisar dattawa a yankin arewa maso yamma zai haifar da ce-ce-ku-ce, sannan yankin kudu maso kudu da yankin kudu maso gabas ba za su lamunta ba, saboda an zabi shugaban kasa musulmi da mataimakinsa musulmi. Haka kuma mukamin shugaban majalisan wakilai ana kai ruwa rana. Tinubu ne kadai zai iya zaben shugabannin majalisu guda biyu tare da kawo karshen ce-ce-ku-ce kan tsarin karba-karba a wurin raba mukamai da daidaiton addini da kuma cusa ra’ayin addini wajen bayar da mukami.

Haka kuma ana tsammanin zababben shugaban kasa ya yi amfani da sauran kwanakin da suka rage masa ya kafa majalisar ministocinsa domin tabbatar da samun nasara bayan ya gaji Shuagaban kasa. Muhammadu Buhari wanda ya shafe watanni shiga kafin iya zakulo mambobin majalisar minintocinsa bayan rantsar da shi a ranar 29 ga watan Mayun 2015, sannan ana tsammanin Tinubu zai kauce wa fadawa irin wannan kuskuren.

LABARAI MASU NASABA

An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

Wani babban kalubalen da Tinubu yake fuskanta shi ne, yadda zai fuskanci cire tallafin man futar wanda za a cire da zai fusata kungiyar kwadugo ta kasa (NLC), wanda suka yi gargadin cire tallafin man. Dokar man nfetur da aka samar a 2022, ta bayyana cewa cire tallafin man da majalisa ta dakatar na tsawon watanni 18, inda zai kare a watan Yuni.

A makon da ya gabata an ji babban sakataren ma’aikatar man fetur, Ambassador Gabriel Aduda cewa an yi la’akari da abubuwa masu yawa wajen tabbatar da cire tallafin mai wanda Tinubu zai fuskanci kalubale, wanda yana cikin alkawarin yakin neman zabe da yadda zai aiwatar da shi ba tare da ya fuskamci bore daga mutane kafin a rantsar da shi.

Zababben shugaban kasa zai kuma fuskanci babban aiki a gabansa wajen tabbatar da sake maido da ingancin rayuwa da zai hada kan ‘yan Nijeriya. A halin yanzu dai, kawunan ‘yan Nijeriya sun rabu ta bangaren akilanci da addini. Hanya daya da zai bi shi ne, tabbatar da adalci da daidaito wajen zaben makarrabansa a majalisar kasa. Haka kuma Tinubu zai fuskanci kalubale wajen wanke kansa kan tuhumar da ake masa a kotunan sauraren karar zabe ga dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar LP, Mista Peter Obi da takwarensa na jam’iyyar PDP, Atilu Abubakar da dai sauransu.

Hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) ta ayyana dan takarar jam’iyyar APC a matsayin wanda ya lashe zaben da ya gudana a ranar 25 ga watan Fabrairu, bayan samunkuri’u 8,794,726. Wanda ya doge abokan hamayyarsa da suka hada da dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP, Atiku da takwaransa na jam’iyyar LP, Obi wadanda suka samu kuri’u 6,984,520 da 6,101,533 a jamlace.

A makon da ta gabata ce Tinubu ya bayyana sunayen mutum 13 a matsayin ‘yan kwamitin amsar mulki a ranar 29 ga watan Mayu. Sai dai kuma PDP ta cacceki Tinubu domin bai nada kowa ba daga yankin kudu maso gabas a cikin mutum 13 da ke cikin kwamitin amsar milki.

Ya dai mika sunayen mutum 13 ne a wata wasika da ke dauke da sa hannun sakataren gwamnatin tarayya, Boss Mustapha, wanda ya bayyana sunayen mutum 13 a matsayin wadanda aka hada a cikin kwamitin amsar mulki.
Kwamitin zai fara aiki ne mako guda kafin rantsarwa wanda zai mika mulki ga Tinubu da mataimakinsa Sanata Kashim Shettima a matsayin shugaban kasa da mataimaki a ranar 29 ga watan Mayu, inda tun da farko aka bayyana sunan Gwamnan Jihar Kebbi, Atiku Bagudu da tsohon kwamishinan kudin Jihar Legas, Wale Edun na daga cikin ‘yan kwamitin.yus

Tinubu
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano
  • Sulaiman
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • Sulaiman
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • Sulaiman
    Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Tinubu
Yusuf Shuaibu
+ posts Bio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

MASU ALAKA

An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano
Labarai

An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

June 25, 2026
Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi
Manyan Labarai

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

June 25, 2026
EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53
Manyan Labarai

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Next Post
Dalibai 947,000 Ne Za Su Rubuta Jarabawar JAMB Cikin Kwanaki 2

Dalibai 947,000 Ne Za Su Rubuta Jarabawar JAMB Cikin Kwanaki 2

LABARAI MASU NASABA

An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

June 25, 2026
APC Ta Dage Yakin Zaben Shugaban Kasarta A Kano

An Dakatar Da Shugaban APC Na Kebbi Da Kwamishina Kan Zaɓen Cike Gurbin Zuru

June 25, 2026
Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

June 25, 2026
EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.