ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Manyan Kalubalen Da Ke Gaban Tinubu Gabanin Rantsar Da Shi

by Sulaiman and Yusuf Shuaibu
3 years ago
Tinubu

Yayin da ya kasnce a ranar 29 ga watan Mayu za a rantsar da zababben Shugaban kasa, Bola Tinubu akwai manyan kalubalen da suke gabansa kafin ya samu nasarar darewa kan karagar mulki.

Daga daga cikin wadannan kalubale ita ce, tsarin karba-karba wurin zaben shugabannin majalisu, wanda an dade ana kai-ruwa-rana a tsaknin mambobin zauren majalisun guda biyu na yadda ake kokarin saka addini da bangarenci ta yadda za a bai wa sashin kudu masu yamma, yayin da wasu ke ganin ya dace a bai wa yankin arewa maso yamma matsayin, saboda yawan kuri’u da zababben shugaban kasa ya samu a wannan yanki.

  • Lafiyata Kalau, Na Shirya Tsaf Don Shugabantar Nijeriya —Tinubu

Haka kuma sababbin mambobin majalisa idanuwansu na kan samun zama shugaban majalisan dattawa, saboda yadda aka zabe su a matsayin ‘yan majalisa a yankunan arewa da kuma na kudu, inda yankin kudu maso gabas ya koko kan yadda bai taba rike wannan kujarar ba. Ana ganin yankin kudu maso kudu ke rige-rige da yankin kudu maso gabas wajen samun mukamin shugabancin majalisan dattawa, domin tabbatar da kirista ya zamanshugaban majalisan dattawa ta yadda za a samu daidaito a tsakanin addinai lasancewa takarar musulmi da musulmi jam’iyyar APC ta yi.

ADVERTISEMENT

Samun shugaban majalisar dattawa a yankin arewa maso yamma zai haifar da ce-ce-ku-ce, sannan yankin kudu maso kudu da yankin kudu maso gabas ba za su lamunta ba, saboda an zabi shugaban kasa musulmi da mataimakinsa musulmi. Haka kuma mukamin shugaban majalisan wakilai ana kai ruwa rana. Tinubu ne kadai zai iya zaben shugabannin majalisu guda biyu tare da kawo karshen ce-ce-ku-ce kan tsarin karba-karba a wurin raba mukamai da daidaiton addini da kuma cusa ra’ayin addini wajen bayar da mukami.

Haka kuma ana tsammanin zababben shugaban kasa ya yi amfani da sauran kwanakin da suka rage masa ya kafa majalisar ministocinsa domin tabbatar da samun nasara bayan ya gaji Shuagaban kasa. Muhammadu Buhari wanda ya shafe watanni shiga kafin iya zakulo mambobin majalisar minintocinsa bayan rantsar da shi a ranar 29 ga watan Mayun 2015, sannan ana tsammanin Tinubu zai kauce wa fadawa irin wannan kuskuren.

LABARAI MASU NASABA

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Wani babban kalubalen da Tinubu yake fuskanta shi ne, yadda zai fuskanci cire tallafin man futar wanda za a cire da zai fusata kungiyar kwadugo ta kasa (NLC), wanda suka yi gargadin cire tallafin man. Dokar man nfetur da aka samar a 2022, ta bayyana cewa cire tallafin man da majalisa ta dakatar na tsawon watanni 18, inda zai kare a watan Yuni.

A makon da ya gabata an ji babban sakataren ma’aikatar man fetur, Ambassador Gabriel Aduda cewa an yi la’akari da abubuwa masu yawa wajen tabbatar da cire tallafin mai wanda Tinubu zai fuskanci kalubale, wanda yana cikin alkawarin yakin neman zabe da yadda zai aiwatar da shi ba tare da ya fuskamci bore daga mutane kafin a rantsar da shi.

Zababben shugaban kasa zai kuma fuskanci babban aiki a gabansa wajen tabbatar da sake maido da ingancin rayuwa da zai hada kan ‘yan Nijeriya. A halin yanzu dai, kawunan ‘yan Nijeriya sun rabu ta bangaren akilanci da addini. Hanya daya da zai bi shi ne, tabbatar da adalci da daidaito wajen zaben makarrabansa a majalisar kasa. Haka kuma Tinubu zai fuskanci kalubale wajen wanke kansa kan tuhumar da ake masa a kotunan sauraren karar zabe ga dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar LP, Mista Peter Obi da takwarensa na jam’iyyar PDP, Atilu Abubakar da dai sauransu.

Hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) ta ayyana dan takarar jam’iyyar APC a matsayin wanda ya lashe zaben da ya gudana a ranar 25 ga watan Fabrairu, bayan samunkuri’u 8,794,726. Wanda ya doge abokan hamayyarsa da suka hada da dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP, Atiku da takwaransa na jam’iyyar LP, Obi wadanda suka samu kuri’u 6,984,520 da 6,101,533 a jamlace.

A makon da ta gabata ce Tinubu ya bayyana sunayen mutum 13 a matsayin ‘yan kwamitin amsar mulki a ranar 29 ga watan Mayu. Sai dai kuma PDP ta cacceki Tinubu domin bai nada kowa ba daga yankin kudu maso gabas a cikin mutum 13 da ke cikin kwamitin amsar milki.

Ya dai mika sunayen mutum 13 ne a wata wasika da ke dauke da sa hannun sakataren gwamnatin tarayya, Boss Mustapha, wanda ya bayyana sunayen mutum 13 a matsayin wadanda aka hada a cikin kwamitin amsar mulki.
Kwamitin zai fara aiki ne mako guda kafin rantsarwa wanda zai mika mulki ga Tinubu da mataimakinsa Sanata Kashim Shettima a matsayin shugaban kasa da mataimaki a ranar 29 ga watan Mayu, inda tun da farko aka bayyana sunan Gwamnan Jihar Kebbi, Atiku Bagudu da tsohon kwamishinan kudin Jihar Legas, Wale Edun na daga cikin ‘yan kwamitin.yus

Tinubu
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo
  • Sulaiman
    Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta
  • Sulaiman
    Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya
  • Sulaiman
    Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa
Tinubu
Yusuf Shuaibu
+ posts Bio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027

MASU ALAKA

Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje
Manyan Labarai

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya
Labarai

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Sabbin Ministoci
Labarai

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
Next Post
Dalibai 947,000 Ne Za Su Rubuta Jarabawar JAMB Cikin Kwanaki 2

Dalibai 947,000 Ne Za Su Rubuta Jarabawar JAMB Cikin Kwanaki 2

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.